• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Na Cikin Tsaka Mai Wuya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Na Cikin Tsaka Mai Wuya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shirin nan na bayar da rance a harkar noma na ‘Anchor Borrowers’, wanda Babban Bankin Nijeriya ya kirkiro tare da jagoranta, domin kara bunkasa harkokin noma a Nijeriya ya fuskanci matukar koma baya, sakamakon kin dawo da kudaden da Manoman suka yi a matsayin rance.

Wannan hali na kin biyan wadannan kudade da wasu daga cikin Manoman da suka amfana da shirin suka yi, ya janyo wa sauran Manoman da ba su amfana da shirin ba tasgaro wajen samun wannan rance, lamarin da ya jefa su cikin tsaka mai wuya.

  • NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo
  • Ma’aikatan Kiwon Lafiya 83 Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Cikin Shekara 8 – MHWUN

Daga cikin Naira tiriliyan 1.1, wanda Babban Bankin Nijeriya ya raba wa Manoma a matsayin rance, tun bayan kafa wannan shiri, kasa da Naira biliyan 546 kacal aka iya dawo da su, inda kimanin Naira biliyan 577 kuma, suka makale a hannun Manoman suka ki maido da su.

Wadannan makudan kudaden, sun makale ne a hannun Bankunan Hada-hadar Kudi, Gwamnatocin Jihohi, Kungiyoyin Manoma, daidaikun mutane, da kuma kamfanoni, wanda hakan ya harzuka Fadar Shugaban Kasa tare da bayyana cewa, hakan ya yi sanadiyyar gaza cimma burin da aka sanya a gaba ainahin manufar shirin.

Wata majiya mai karfi, ta sheda wa Jaridar Banguard cewa, an yi wa Shugaba Kasa Bola Ahmed Tinubu bayani a kan lamarin, inda ya yi matukar nuna bacin ransa a kan wadanda suka amfana da shirin suka kuma ki maido da wadannan kudade da aka ba su a matsayin rance. A cewar tasa, da sun maido da wadannan kudade, akwai yiwuwar wadanda ba su samu ba, su ma su samu.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Bugu da kari, daya daga cikin hukumomin tsaron ya bayyana cewa, Tinubu ya umarci daukan dukkanin matakan da suka dace na dawo da wadannan kudade daga wurin wadanda suka amfana da su, suka kuma ki maidowa daga nan zuwa ranar 18 ga watan Satumban 2023, musamman domin ainahin Manoman su amfana da su, a samu wadataccen abinci a fadin wannan kasa.

Haka zalika, an kuma shaida wa shugaban kasar cewa, Babban Bankin Nijeriya tare da ‘yan barandansa, sun karkatar da kimanin Naira miliyan 255, wadanda ya kamata a rabawa wa sauran Manoman da ba su samu ba.

Bugu da kari, an sake zargin bankuna da sauran wasu kungiyoyi a matsayin wadanda suka karkatar da naira miliyan 255, da aka karbo daga wurin wadanda suka amfana da wannan rance, amma suka ki mika wa Babban Bankin wadannan kudade.

Har ila yau, wasu daga cikin wadanda suka amfana da rancen kudaden, sun ki maido da su ne tare da yin ikirarin cewa, sun yi noman amma ba su samu wata rabar a zo a gani ba, inda suke sake bukatar a kara musu wani wa’adin, domin mayar da rance ga Babban Bankin Nijeriyar.

Tuni dai jami’ain tsaro suka fara tuhumar wasu daga cikin Manajojin Bankuna da dama a kan rikita-rikitar ta kin maido da wadannan kudade na rance, wanda akasarinsu sun amsa saba ka’idar da aka ginidaya ta maido da rancen kudaden.

Wasu daga cikin kungiyoyin da suka amfana da rancen a karkashin shirin na ‘Anchor Borrowers’, sun hada da Kungiyar Manoman Masara, Waken Suya da kuma Noman Auduga.

Kazalika, binciken Jaridar Banguard din ya sake nuna cewa, Kungiyar Manoman Masara ta karbi rancen naira  biliyan 39 daga Babban Bankin Nijeriya, a karkashin wannan shiri na ‘Anchor Borrowers’.

Haka nan ita ma, Kungiyar Manoman Auduga ta karbi rancen naira biliyan 14, sannan ta maido da naira biliyan 5 daga ciki.

Har wa yau, an yi kokarin jin ta bakin mai magana da yawun Hukumomin Tsaro da ke Abuja a kan umarnin da Shugaban Kasar ya bayar  na karbo wadannan kudade, amma bai ce komai ba.

Haka nan, shi ma Kakakin Hukumar Tsaro ta farin kaya (DSS), Dakta  Peter Afunanya; da aka tuntube shi don jin ta bakinsa, bai ce uffan ba, sai dai ya ce, batun bayar da umarnin Shugaban Kasa; ba wani sabon abu ne ga Hukomin Tsaron Kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Farin Ciki Ya Lullube Manoma A Taraba Sakamakon Tashin Farashin Agushi

Next Post

Xi Ya Jaddada Yin Kokari Wajen Farfado Da Yankin Arewa Maso Gabashin Kasar Sin

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

2 weeks ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

4 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

4 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 month ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 month ago
Next Post
Xi

Xi Ya Jaddada Yin Kokari Wajen Farfado Da Yankin Arewa Maso Gabashin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Bashin

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.