• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Na Cikin Tsaka Mai Wuya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Na Cikin Tsaka Mai Wuya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shirin nan na bayar da rance a harkar noma na ‘Anchor Borrowers’, wanda Babban Bankin Nijeriya ya kirkiro tare da jagoranta, domin kara bunkasa harkokin noma a Nijeriya ya fuskanci matukar koma baya, sakamakon kin dawo da kudaden da Manoman suka yi a matsayin rance.

Wannan hali na kin biyan wadannan kudade da wasu daga cikin Manoman da suka amfana da shirin suka yi, ya janyo wa sauran Manoman da ba su amfana da shirin ba tasgaro wajen samun wannan rance, lamarin da ya jefa su cikin tsaka mai wuya.

  • NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo
  • Ma’aikatan Kiwon Lafiya 83 Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Cikin Shekara 8 – MHWUN

Daga cikin Naira tiriliyan 1.1, wanda Babban Bankin Nijeriya ya raba wa Manoma a matsayin rance, tun bayan kafa wannan shiri, kasa da Naira biliyan 546 kacal aka iya dawo da su, inda kimanin Naira biliyan 577 kuma, suka makale a hannun Manoman suka ki maido da su.

Wadannan makudan kudaden, sun makale ne a hannun Bankunan Hada-hadar Kudi, Gwamnatocin Jihohi, Kungiyoyin Manoma, daidaikun mutane, da kuma kamfanoni, wanda hakan ya harzuka Fadar Shugaban Kasa tare da bayyana cewa, hakan ya yi sanadiyyar gaza cimma burin da aka sanya a gaba ainahin manufar shirin.

Wata majiya mai karfi, ta sheda wa Jaridar Banguard cewa, an yi wa Shugaba Kasa Bola Ahmed Tinubu bayani a kan lamarin, inda ya yi matukar nuna bacin ransa a kan wadanda suka amfana da shirin suka kuma ki maido da wadannan kudade da aka ba su a matsayin rance. A cewar tasa, da sun maido da wadannan kudade, akwai yiwuwar wadanda ba su samu ba, su ma su samu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Bugu da kari, daya daga cikin hukumomin tsaron ya bayyana cewa, Tinubu ya umarci daukan dukkanin matakan da suka dace na dawo da wadannan kudade daga wurin wadanda suka amfana da su, suka kuma ki maidowa daga nan zuwa ranar 18 ga watan Satumban 2023, musamman domin ainahin Manoman su amfana da su, a samu wadataccen abinci a fadin wannan kasa.

Haka zalika, an kuma shaida wa shugaban kasar cewa, Babban Bankin Nijeriya tare da ‘yan barandansa, sun karkatar da kimanin Naira miliyan 255, wadanda ya kamata a rabawa wa sauran Manoman da ba su samu ba.

Bugu da kari, an sake zargin bankuna da sauran wasu kungiyoyi a matsayin wadanda suka karkatar da naira miliyan 255, da aka karbo daga wurin wadanda suka amfana da wannan rance, amma suka ki mika wa Babban Bankin wadannan kudade.

Har ila yau, wasu daga cikin wadanda suka amfana da rancen kudaden, sun ki maido da su ne tare da yin ikirarin cewa, sun yi noman amma ba su samu wata rabar a zo a gani ba, inda suke sake bukatar a kara musu wani wa’adin, domin mayar da rance ga Babban Bankin Nijeriyar.

Tuni dai jami’ain tsaro suka fara tuhumar wasu daga cikin Manajojin Bankuna da dama a kan rikita-rikitar ta kin maido da wadannan kudade na rance, wanda akasarinsu sun amsa saba ka’idar da aka ginidaya ta maido da rancen kudaden.

Wasu daga cikin kungiyoyin da suka amfana da rancen a karkashin shirin na ‘Anchor Borrowers’, sun hada da Kungiyar Manoman Masara, Waken Suya da kuma Noman Auduga.

Kazalika, binciken Jaridar Banguard din ya sake nuna cewa, Kungiyar Manoman Masara ta karbi rancen naira  biliyan 39 daga Babban Bankin Nijeriya, a karkashin wannan shiri na ‘Anchor Borrowers’.

Haka nan ita ma, Kungiyar Manoman Auduga ta karbi rancen naira biliyan 14, sannan ta maido da naira biliyan 5 daga ciki.

Har wa yau, an yi kokarin jin ta bakin mai magana da yawun Hukumomin Tsaro da ke Abuja a kan umarnin da Shugaban Kasar ya bayar  na karbo wadannan kudade, amma bai ce komai ba.

Haka nan, shi ma Kakakin Hukumar Tsaro ta farin kaya (DSS), Dakta  Peter Afunanya; da aka tuntube shi don jin ta bakinsa, bai ce uffan ba, sai dai ya ce, batun bayar da umarnin Shugaban Kasa; ba wani sabon abu ne ga Hukomin Tsaron Kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Farin Ciki Ya Lullube Manoma A Taraba Sakamakon Tashin Farashin Agushi

Next Post

Xi Ya Jaddada Yin Kokari Wajen Farfado Da Yankin Arewa Maso Gabashin Kasar Sin

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

3 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

10 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Xi

Xi Ya Jaddada Yin Kokari Wajen Farfado Da Yankin Arewa Maso Gabashin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Bashin

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.