• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Bincike ya nuna cewa, duk da tsadar kayan aikin noman rani a bana, da manoman shinkfa da na alkama ke fuskanata a jihar Taraba, sun nuna cewa za su samu amfani mai yawa a bana.

Manoman a fadin jihar, sun bayyana cewa, suna sa ran samun amfani mai yawa na wadannan amfanin nan da mako mai zuwa.

  • Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun
  • Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana

Za a fara diban amfanin gonar biyu ne nan da mako biyu a kananan hukumomi Karim-Lamido da Gassol da Lau da Donga, inda za a yankin Shika, fiye da manoma 200 da suka shuka shinkafa sun fara yankanta.

Rahotannin sun nuna cewa, kashi 60 daga cikin dari na gonakin da aka shuka wadannan amfanin biyu, sun kai munzalin fara dibansu, inda moman na ke da yakinin samun amfani mai dimbin yawa, duk da cewa, sun samu kalubalen dizil da man fetur da suke zuba wa a cikin ijinan ban- ruwansu.

Daya daga cikin manoman ranin mai suna Injiya Yahaya Mafindi, ya bayyana cewa, gonarsa ta shinkfa ta fada cikin ambaliyar ruwan a shekarar da ta wuce, saboda haka ta lalatace, hakan ya sa ya fara yin noman rani da wuri a bana, inda ya ce, nan da mako uku yake sa ran yanke shinkafarsa.

Kashi 60 daga cikin dari na gonakin da aka shuka wadannan amfanin biyu, sun kai munzalin a fara dibansu, inda manoman, ke da yakinin samun amfani mai yawa, duk da cewa, sun samu kalubalen dizil da man fetur da muke zuba wa a cikin ijinan ban-ruwa.

Mafindi ya ci gaba da cewa, da farko ya samu rashin kwarin gwiwa da zai fara yin noman na rani, saboda tsadar man fetur da zai zuba a cikin injin ban-ruwa da zai yi amfani da shi a gonarsa.

A cewarsa, yana da injinan ban-ruwa guda uku da yake yin amfani da su don yin ban-ruwa a gonarsa, amma saboda tsadar man fetur, hakan ya sa ya sayo injinan ban-ruwa mai aiki da hasken rana, inda ya shawarci manoman kar su fara tunin yin noman rani a bana idan sun san ba su da isasun kudin da za su sayi man fetur da iri da magungunna feshi da sauransu.

Shi ma wani manoman na rani mai suna Yakubu Dauda, ya bayyana cewa, kashi 50 daga cikin dari na noman rani da ya yi, ya karbo rancen naira 500, 000 a bana, inda ya kara da cewa, yana sa ran samun shinkafar mai yawa.

Sannan kuma, ya nuna jin dadinsa kan rashin kwarin da ke lalata shinkafar da aka shuka sabanin yadda ta auku a shekarar da ta wuce, musamman a karamar hukumar Lau da Karim-Lamido da Gassol, inda ya kara da cewa, kalubalen da manoman suka fuskanta a wannan shekarar shi ne kawai na tsadar man dizill da na man feutur da suke zuba wa injinan ban-ruwa.

Wani manomin shi ma mai suna Alhaji Isa Tafida, wanda yake bai wa manoman rani rancen kudin yin noman na rani a lokacin aikin shinkafa, ya bayyana cewa, yana bayar da rancen ne kashi 50 a cikin dari, musamman ga manoman da suka yi asara saboda ambaliyar ruwan da ta auku a shekarar da ta wuce a yankin, don su sake farafado wa.

Ya kuma ci gaba da cewa, da alaumun manoman na rani a yankin, bana za su samu amfani mai dimbin yawa, inda ya nuna jin dadinsa kan yadda mnoman za su sake fafrfado wa biyo bayan aukuwar ambaliyar ruwan.

“Na bayar da rancen ne kashi 50 daga cikin dari, musamman ga manoman da suka yi asara saboda ambaliyar ruwan da ta auku a shekarar da ta wuce a yankin, musamman don su sake farafadowa.”

A yankunan Tau da kuma Didango da ke a kananan hukumomin Ardo-Kola da Karim-Lamido akasarin manoman na shinkafar da alkamar da aka tattauan da su sun bayyana cewa, suna sa ran  samun amfani mai dimbin yawa.

Daya daga cikinsu, mai suna, Musa Didango ya bayyana cewa, koda yake sun samu kalubalen tsadar kayan aikin na yin noman rani, amma mun ji dadi sosai saboda wa su kalubalen da suka samu na kwarin da ke lalata amfanin gona da kuma na makiyayan da ke tura dabbobinsu cikin gonakinsu.

“Mun ji dadi sosai saboda ba mu fuskanci kalubalen kwarin da ke lalata amfanin gona ba da kuma na makiyayan da ke tura dabbobinsu cikin gonakinmu ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ManomaShinkafaTaraba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana

Next Post

Hafsan Hafsoshin Soji Na Zamanin Abacha, Laftanar Janar Diya, Ya Rasu

Related

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

2 days ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

1 week ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

1 week ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Next Post
Hafsan Hafsoshin Soji Na Zamanin Abacha, Laftanar Janar Diya, Ya Rasu

Hafsan Hafsoshin Soji Na Zamanin Abacha, Laftanar Janar Diya, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

July 28, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

July 28, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

July 28, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10

July 28, 2025
An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

July 28, 2025
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

July 28, 2025
Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.