ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana

by SP. Imam Ahmad Kutubi
3 years ago
Azumi

Assalamu alaikum warahmatullahi wa barakatuhu. Mun Fara Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai, Dukkan Yabo Da Godiya Sun Tabbata Ga Allah Ubangijin Talikai, Tsira Da Amincin Allah Su Kara Tabbata Ga Shugabanmu Annabi Muhammad Da Iyalansa Da Sahabbansa Baki Daya.

Da farko muna wa kowa da kowa barka da shiga wannan wata mai alfarma na Azumin Ramadan. Da fatan Allah ya karbi ibadunmu, Allah ya sa muna daga cikin wadanda za a ‘yanta.

  • Zaben Gwamna: PDP Za Ta Yi Zanga-Zangar Kwana 7 Kan Sakamakon Zaben Nasarawa 
  • ‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023

Shi dai Azumin watan ramadana farilla ne, yana daga cikin shikashikan musuluncin nan biyar. Wanda ya yi niyyarsu tun a cikin daren farko na ramadana, niyyar nan guda ta wadatar domin azumin watan ramadana dukkansa. Idan mace ta shafa tozali tun gabanin alfijir, ko kuma mutum ya saka magani a cikin hancinsa, to ko maganin nan ya gangaro ga makogaro da rana azumi bai karye ba. Idan kuwa ya karya shi ne da gangan, ko kuwa ya di daukarsa ba da wani uzuri ba, to zai rama shi ta kowane hali, sannan kuma ya kara da yin kaffara. An halatta wa matafiyi, tafiya irin wadda ta hallata a gajarta sallah dominta, ya sha azumi, amma ya yi ramuwa. Mai itikafi ba zai fita masallaci don gai da marasa lafiya ba, sai idan dayan iyayensan ne. Kuma ba zai fita don sallah a kan mamaci ko don yin ciniki ba.

ADVERTISEMENT

Ma’anar Azumi

Azumi shi ne kamewa daga dukkan abin da ciki da farji ko zakari suke sha’awarsa, tun daga alfijir har zuwa faduwar rana da niyyar yin ibada.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Azumin watan ramadana farilla ne, yana daga cikin shikashikan musulunci guda biyar.

Tabbatar Tsayuwar Wata

Tsayuwar watan ramadana yana tabbata da samuwar daya daga cikin abubuwan nan biyu da za mu ambata; Ganin sabon watan ramadan da ido, a ranar da sha’aban ya cika kwana ashirin da tara. To, idan mutum biyu adalai suka ga wata da idanunsu, azumi ya wajaba ga dukan wanda ya sami labarin ganin wata. Adali shi ne wanda baya aikata manya zunubai Kuma yana kokari ga barin kananan zunubai da galib6insu.

Haka kuma kama azumi yana wajaba idan taron mutane da yawa wadanda ba adilai ba suka ce sun ga wata, alhali kuma don yawansu har ba ya yiwuwa a ce ko sun hada kai ne don su fadi karya. Amma idan mutum guda daya ne ya ga wata, ba za a kama azumi domin ganinsa shi kadai ba ko da kuwa ya fi mutanen duniya gaskiya da adalci. Amma shi wanda ya ga wata ko da ba adali ba ne wajibi ne a kansa ya dauki azumi tare da shi da iyalansa kadai, sauran mutane kuwa ba ruwansu.

Kuma wajibi ne a kan wanda duk ya ga wata ko da fasiki ne, ya je gun sarki ko shugabannin addini na garinsu ya sanar.

Idan an ga wata a wata kasa mai nisa can gabas, idan mutanen wata kasa ta yamma da su suka sami labari daga garesu, a wani kauli na malamai ya halatta su dauki azumi tare da su, a wani kauli kuma bai halatta ba sai dai idan duk malamai sun yi ittifa’ki cewa idan tsakaninsu akwai nisa kwarai bai halatta su yi koyi da su ba. Kamar tsakanin indiya da spain.

Dalili na biyu wanda zai tabbatar da tsayuwar watan ramadana shi ne cikar watan sha’aban kwana talatin cif. To, ko da ba a ga watan ramadana ba sai a yi azumi hakan.

Dalilin da aka bi don tabbar da tsayuwar watan ramadan su ne kuma za a yi aiki da su don tabbatar da tsayuwar watan shawwal. Wato watan karamar sallah.

Sharuddan Wajibcin Azumi Da Ingancinsa

 Sharuddansa Bakwai Ne (7)

Niyya: Wajibi ne mutum ya yi niyya ya ce; Nayi niyyar yin azumin watan Ramadana, farilla. Tun daga faduwar rana har zuwa fitowar alfijir duk lokaci ne na yin niyya. Amma ana fadan haka ne a cikin zuciya. Wanda ya yi niyyarsa tun a cikin daren farko na Ramadana, niyyar nan guda ta wadatar domin azumin watan Ramadana har ya gama dukkansa. Amma da sharadin kwanakin azuminsa su bi juna, ba su yanke ba. Idan ko da kwana daya ne ya baci, ko kuma bai dauki azumi a cikinsa ba don rashin lafiya, ko tafiya, ko haila ko jinin biki, to wajibi ne ya sake wata sabuwar niyya domin ragowar kwanakin Ramadana. Ya hallata ga wanda ya yi niyya tun da magriba a kan ya ci, ya sha, ya yi jima’i da matarsa har zuwa alfijir. Wanda bai yi niyya ba tun daren farko na ganin wata to ba shi da azumi.

Tsarki Daga Jinin Haila Ko Jinin Biki: Mace mai haila ko jinin biki ba za ta yi azumi ba, kuma ba za ta yi salla ba. Amma za ta rama dukkan azumin da ta sha, ban da sallah. Ba za ta rama sallah ba. Ya wajaba ga mace mai haila ko jinin biki ta duba farjinta da ‘yar auduga, ko farin kyalle a kusan fitowar alfijir, don ta gani ko azumin gobe zai wajaba a kanta, za ta yi haka ne saboda ta gane ko jinin ya tsaya.

Hankali: Babu azumi akan mahaukaci, kuma bai inganta ba, amma zai rama dukkan azumin da ya sha bayan warkewarsa.

Balaga: Azumi bai wajaba a kan yaro ko yarinya wadanda ba su balaga ba.

Musulunci; Babu azumi a kan kafiri.

Samun Iko: Azumi bai wajaba ba a kan wanda ba ya iya yinsa domin ciwon kishirwa ko ciwon yunwa ko don tsufa tukuf.

Barin Yin Jima’i Ko Fitar Da Maniyyi, Ko Maziyyi Da Rana, Da Barin Shigar Da Wani Abu A Cikin Ciki Da Rana:  Wanda ya yi daya daga cikin wadannan babu azuminsa. Mutum ko da tsakuwa ce ya hadiye har ta kai ciki, azuminsa ya karye. Idan kuwa abu ruwa-ruwa ne, da ya kai ga makogoro, shikenan azumi ya karye don ba ya yiwuwa ya maido shi baya. Kofofin jiki wadanda idan wani abu ya shiga ta cikinsu har ya kai ciki azumi zai karye shida ne kawai. Su ne: Baki, hanci, idanu, kunnuwa, dubura da farjin mace. Dura magani ko wani abu ta kofar zakari ko ta wani kurji mai zurfi daura da ciki ba zai karya azumi ba kamar misali (yin Allura).

Haka kuma idan mace ta shafa tozali tun gabanin alfijir ko kuma mutum ya saka magani a cikin hancinsa, to, ko maganin ya gangaro ga makogoro da rana, azumi bai karye ba. Abin da dai aka hana shi ne aikata dayan wadannan bayan fitowar alfijir, wannan kam azumi zai karye idan sun gangaro ga makogwaro.

Azumi
SP. Imam Ahmad Kutubi
+ postsBio
  • SP. Imam Ahmad Kutubi
    https://hausa.leadership.ng/author/sp-imam-ahmad-kutubi/
    Hukunce-Hukuncen Sallar Idi Da Zakatul Fidir
  • SP. Imam Ahmad Kutubi
    https://hausa.leadership.ng/author/sp-imam-ahmad-kutubi/
    Yadda Ake Ittikafi Da Kuma Hukunce-Hukuncensa
  • SP. Imam Ahmad Kutubi
    https://hausa.leadership.ng/author/sp-imam-ahmad-kutubi/
    Karya Azumi Da Hukunce-hukuncensa
  • SP. Imam Ahmad Kutubi
    https://hausa.leadership.ng/author/sp-imam-ahmad-kutubi/
    Hukunce-hukuncen Sallar Idi Da Layya (Fatawa)

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba

Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.