• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marigayiya Hajiya Murja Bara’u Mangal: Uwa Tagari

by Leadership Hausa
3 years ago
in Rahotonni
0
Marigayiya Hajiya Murja Bara’u Mangal: Uwa Tagari

Marigayiya Hajiya Bara'u Mangal

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu iya magana na cewa mai son dan kwarai, ya auri isassa. Wannan falsafa daga kundin hikimomin Malam Bahaushe, ba ma za ta saidu kawai ba ne ga sauran al’ummomi.

Har ma za a iya yin na’am daya bawa da ita. Domin kuwa duk inda ka gadan kirki, daga kuma kowace irin al’umma ya fito, to kuwa babu shakka da ka bincika, zaka samu cewa ya samu tarbiya ta gari.

  • Yadda Za Ki Gane Yanayin Fatarki
  • Yaya Ake Gane Alamomin Mutum Ya Yi Kyakykyawan Karshe?

Kaso mai tsoka kuwa na samun tarbiya ta gari daga uwa ake samunta. Domin kuwa ita ce ke tare da shi, take kuma kula tare da auna kowane irin motsi nasa tun daga kuruciya har girmansa.

Wannan ga kowane gama garin mutum kenan. Ga Alhaji Dahiru Mangal, abin ya zarce haka. Domin kuwa yayarsa Hajiya Hauwa ta tabbatar mani da cewa alakar Alhaji Dahiru Bara’u Mangal da mahaifiyarsa ta zarce duk yadda ake tsammani.

Domin kuwa a kowace rana ta Allah, idan ya fito daga gidansa gidan mahaifiyarsa yake soma zuwa ya gaishe ta.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Idan kuwa har wata hidima wadda ke da lokaci ta rutsa da shi, kamar daurin aure da makamancinsa, to kuwa idan ma har ya wuce bai samu zuwa ya gaishe ta ba, to kuwa daga can gidanta zai zarce.

Haka kuma, idan ya yi tafiya ya dawo, gidanta ya ke soma zuwa kafin ya wuce gidansa. Sai dai ko idan da daddare ya dawo.

Ba gaisuwa kawai ke kai Alhaji Dahiru Mangal ga mahaifiyarsa ba, har da sauraren bukatunta domin ya biya mata.

Yana kuma jin linzaminta yadda ya kamata. Yana tsayawa cak, inda ta tsaida shi. Ya kuma ruga inda ta aike shi. Ma’ana dai bai hada ta da komai ba. Maganarta ita ce ta karshe. Kuma ko ya takura, huskarsa ba ta nuna takurar.

 Wasu na hasashen cewa wannan ne ma sirrin nasararsa. Ta yadda yake samun nasara ga dukkan abubuwan da ya tunkara a rayuwa.

Malam Abbate wani dattijon Malami a garin Katsina wanda kuma ya rage daga cikin abokan Alhaji Bara’u wato Mahaifin Alhaji Dahiru Mangal ya bayyana mani cewa Alhaji Dahiru Mangal ya gaji wannan kyautatawa da yake yi wa Mahaifiyar tasa ne daga Kakansa Alhaji Tukur, wanda ya kan je ya gaida mahaifiyarsa, wadda ake cewa Done, a kowace rana.

Malam Abbate ya kara da cewa “Shi ma Mahaifinsa Alhaji Bara’u ya kan zo gaishe da wannan tsohuwa da kuma kawo mata abinci. Ta haka ne ma muka saba da juna, har muka zama aminan juna.

Da yake gidanta yana makwabtaka da gidanmu. Don haka, duk lokacin da ya zo ya kan shiga ya gaishe da Shehi (Mahaifinsu).”

An haifi Hajiya Murja Muhammad Dodoa shekarar 1937. Mahaifinta shi ne Alhaji Dodon Kanti.

Ita ce diyarsa ta biyu. Ta yi aure tun tana da shekara goma sha ukku (13) a duniya, a shekarar 1950.

Ta haifi ‘ya’ya takwas, hudu maza, hudu mata. Mazan su ne Alhaji Dahiru Bara’u Mangal (na farko a cikin maza, na biyu a haihuwa) da Marigayi Alhaji Muntari da Alhaji Bishir da kuma Marigayi Alhaji Marwana.

A lokacin da matan sukakasance Hajiya Hauwa (ta farko a haihuwa)da Marigayiya Hajiya Mariya da Hajiya Zulai da kuma Marigayiya Hajiya Nana Bilkisu.

Wato hudu daga cikin su ne ke raye. Biyu maza, biyu mata. Mazan su ne Alhaji Dahiru Bara’u Mangal da Alhaji Bishir Bara’uMangal.

A lokacin da matan suka kasance Hajiya Hauwa Bara’u Mangal da Hajiya Zulai Bara’u Mangal.

Hajiya Murja na daukar nauyin mutane da dama zuwa aikin Hajji da Umra, musamman ma aminanta da ‘yan’uwa da abokan arziki.

Kuma dukkan nauyi take daukewa ba tare da rage komai ga wanda ta dauki nauyinsa. Kusan dukkan tafiya-tafiyen da take yi, musamman ma aikin Hajji da umra tare take yinsu da Babbar kawarta, kuma aminiyarta ta kusa Hajiya ‘Yarbaba.

Marubucin wannan mukala ya jinjina masaa lokacin da wani abokinsa Alhaji Magaji Abdullahi Kankiya ya sheda masa cewa a lokacin da ya je aikin Hajji sun zo filin jirgiza su dawo gida a Jirgin Mad Air sai suka iske Hajiya (mahaifiyar Alhaji Dahiru Mangal) ta riga ta shiga jirgin ita ma za a dawo da ita.

Irin yadda ya ga baki dayan ma’aikatan jirgin na kazar-kazar da ~arin jikin ganin fasinjojin jirgin sun shiga jirgin a cikin gaugawa, domin kada a bata mata lokaci.

Lamarin da ya sa Alhaji Magajin ya sheda irin tsabar girmamawar da Alhaji Dahiru Mangal ke yi wa mahaifiyarsa. Wanda kuma ga shi har hakan ya yi naso ga ma’aikatansa.

Allah Ya jikanta da rahma. Ya girmama lada. Ya kuma sa Jannatul Firdausi ta zama makomarta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AttajiriBiyayyaHajiya Bara'uKatsinaMahaifiyaMangal
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalubalen Da Ke Gaban Sabon Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasa

Next Post

Muna Bukatar Tallafin Gwamnati Don Bunkasa Noma A Garin Gwanda -Mai Unguwa Yahuza

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

4 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 week ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

1 week ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Next Post
Muna Bukatar Tallafin Gwamnati Don Bunkasa Noma A Garin Gwanda -Mai Unguwa Yahuza

Muna Bukatar Tallafin Gwamnati Don Bunkasa Noma A Garin Gwanda -Mai Unguwa Yahuza

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da ÆŠumi-É—umi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
ÆŠan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

ÆŠan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.