ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marigayiya Hajiya Murja Bara’u Mangal: Uwa Tagari

by Leadership Hausa
3 years ago
Marigayiya Hajiya Bara'u Mangal

Marigayiya Hajiya Bara'u Mangal

Masu iya magana na cewa mai son dan kwarai, ya auri isassa. Wannan falsafa daga kundin hikimomin Malam Bahaushe, ba ma za ta saidu kawai ba ne ga sauran al’ummomi.

Har ma za a iya yin na’am daya bawa da ita. Domin kuwa duk inda ka gadan kirki, daga kuma kowace irin al’umma ya fito, to kuwa babu shakka da ka bincika, zaka samu cewa ya samu tarbiya ta gari.

  • Yadda Za Ki Gane Yanayin Fatarki
  • Yaya Ake Gane Alamomin Mutum Ya Yi Kyakykyawan Karshe?

Kaso mai tsoka kuwa na samun tarbiya ta gari daga uwa ake samunta. Domin kuwa ita ce ke tare da shi, take kuma kula tare da auna kowane irin motsi nasa tun daga kuruciya har girmansa.

ADVERTISEMENT

Wannan ga kowane gama garin mutum kenan. Ga Alhaji Dahiru Mangal, abin ya zarce haka. Domin kuwa yayarsa Hajiya Hauwa ta tabbatar mani da cewa alakar Alhaji Dahiru Bara’u Mangal da mahaifiyarsa ta zarce duk yadda ake tsammani.

Domin kuwa a kowace rana ta Allah, idan ya fito daga gidansa gidan mahaifiyarsa yake soma zuwa ya gaishe ta.

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Idan kuwa har wata hidima wadda ke da lokaci ta rutsa da shi, kamar daurin aure da makamancinsa, to kuwa idan ma har ya wuce bai samu zuwa ya gaishe ta ba, to kuwa daga can gidanta zai zarce.

Haka kuma, idan ya yi tafiya ya dawo, gidanta ya ke soma zuwa kafin ya wuce gidansa. Sai dai ko idan da daddare ya dawo.

Ba gaisuwa kawai ke kai Alhaji Dahiru Mangal ga mahaifiyarsa ba, har da sauraren bukatunta domin ya biya mata.

Yana kuma jin linzaminta yadda ya kamata. Yana tsayawa cak, inda ta tsaida shi. Ya kuma ruga inda ta aike shi. Ma’ana dai bai hada ta da komai ba. Maganarta ita ce ta karshe. Kuma ko ya takura, huskarsa ba ta nuna takurar.

 Wasu na hasashen cewa wannan ne ma sirrin nasararsa. Ta yadda yake samun nasara ga dukkan abubuwan da ya tunkara a rayuwa.

Malam Abbate wani dattijon Malami a garin Katsina wanda kuma ya rage daga cikin abokan Alhaji Bara’u wato Mahaifin Alhaji Dahiru Mangal ya bayyana mani cewa Alhaji Dahiru Mangal ya gaji wannan kyautatawa da yake yi wa Mahaifiyar tasa ne daga Kakansa Alhaji Tukur, wanda ya kan je ya gaida mahaifiyarsa, wadda ake cewa Done, a kowace rana.

Malam Abbate ya kara da cewa “Shi ma Mahaifinsa Alhaji Bara’u ya kan zo gaishe da wannan tsohuwa da kuma kawo mata abinci. Ta haka ne ma muka saba da juna, har muka zama aminan juna.

Da yake gidanta yana makwabtaka da gidanmu. Don haka, duk lokacin da ya zo ya kan shiga ya gaishe da Shehi (Mahaifinsu).”

An haifi Hajiya Murja Muhammad Dodoa shekarar 1937. Mahaifinta shi ne Alhaji Dodon Kanti.

Ita ce diyarsa ta biyu. Ta yi aure tun tana da shekara goma sha ukku (13) a duniya, a shekarar 1950.

Ta haifi ‘ya’ya takwas, hudu maza, hudu mata. Mazan su ne Alhaji Dahiru Bara’u Mangal (na farko a cikin maza, na biyu a haihuwa) da Marigayi Alhaji Muntari da Alhaji Bishir da kuma Marigayi Alhaji Marwana.

A lokacin da matan sukakasance Hajiya Hauwa (ta farko a haihuwa)da Marigayiya Hajiya Mariya da Hajiya Zulai da kuma Marigayiya Hajiya Nana Bilkisu.

Wato hudu daga cikin su ne ke raye. Biyu maza, biyu mata. Mazan su ne Alhaji Dahiru Bara’u Mangal da Alhaji Bishir Bara’uMangal.

A lokacin da matan suka kasance Hajiya Hauwa Bara’u Mangal da Hajiya Zulai Bara’u Mangal.

Hajiya Murja na daukar nauyin mutane da dama zuwa aikin Hajji da Umra, musamman ma aminanta da ‘yan’uwa da abokan arziki.

Kuma dukkan nauyi take daukewa ba tare da rage komai ga wanda ta dauki nauyinsa. Kusan dukkan tafiya-tafiyen da take yi, musamman ma aikin Hajji da umra tare take yinsu da Babbar kawarta, kuma aminiyarta ta kusa Hajiya ‘Yarbaba.

Marubucin wannan mukala ya jinjina masaa lokacin da wani abokinsa Alhaji Magaji Abdullahi Kankiya ya sheda masa cewa a lokacin da ya je aikin Hajji sun zo filin jirgiza su dawo gida a Jirgin Mad Air sai suka iske Hajiya (mahaifiyar Alhaji Dahiru Mangal) ta riga ta shiga jirgin ita ma za a dawo da ita.

Irin yadda ya ga baki dayan ma’aikatan jirgin na kazar-kazar da ~arin jikin ganin fasinjojin jirgin sun shiga jirgin a cikin gaugawa, domin kada a bata mata lokaci.

Lamarin da ya sa Alhaji Magajin ya sheda irin tsabar girmamawar da Alhaji Dahiru Mangal ke yi wa mahaifiyarsa. Wanda kuma ga shi har hakan ya yi naso ga ma’aikatansa.

Allah Ya jikanta da rahma. Ya girmama lada. Ya kuma sa Jannatul Firdausi ta zama makomarta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
Rahotonni

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Next Post
Muna Bukatar Tallafin Gwamnati Don Bunkasa Noma A Garin Gwanda -Mai Unguwa Yahuza

Muna Bukatar Tallafin Gwamnati Don Bunkasa Noma A Garin Gwanda -Mai Unguwa Yahuza

LABARAI MASU NASABA

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.