• English
  • Business News
Wednesday, May 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marigayiya Hajiya Murja Bara’u Mangal: Uwa Tagari

by Leadership Hausa
3 years ago
in Rahotonni
0
Marigayiya Hajiya Murja Bara’u Mangal: Uwa Tagari

Marigayiya Hajiya Bara'u Mangal

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu iya magana na cewa mai son dan kwarai, ya auri isassa. Wannan falsafa daga kundin hikimomin Malam Bahaushe, ba ma za ta saidu kawai ba ne ga sauran al’ummomi.

Har ma za a iya yin na’am daya bawa da ita. Domin kuwa duk inda ka gadan kirki, daga kuma kowace irin al’umma ya fito, to kuwa babu shakka da ka bincika, zaka samu cewa ya samu tarbiya ta gari.

  • Yadda Za Ki Gane Yanayin Fatarki
  • Yaya Ake Gane Alamomin Mutum Ya Yi Kyakykyawan Karshe?

Kaso mai tsoka kuwa na samun tarbiya ta gari daga uwa ake samunta. Domin kuwa ita ce ke tare da shi, take kuma kula tare da auna kowane irin motsi nasa tun daga kuruciya har girmansa.

Wannan ga kowane gama garin mutum kenan. Ga Alhaji Dahiru Mangal, abin ya zarce haka. Domin kuwa yayarsa Hajiya Hauwa ta tabbatar mani da cewa alakar Alhaji Dahiru Bara’u Mangal da mahaifiyarsa ta zarce duk yadda ake tsammani.

Domin kuwa a kowace rana ta Allah, idan ya fito daga gidansa gidan mahaifiyarsa yake soma zuwa ya gaishe ta.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Idan kuwa har wata hidima wadda ke da lokaci ta rutsa da shi, kamar daurin aure da makamancinsa, to kuwa idan ma har ya wuce bai samu zuwa ya gaishe ta ba, to kuwa daga can gidanta zai zarce.

Haka kuma, idan ya yi tafiya ya dawo, gidanta ya ke soma zuwa kafin ya wuce gidansa. Sai dai ko idan da daddare ya dawo.

Ba gaisuwa kawai ke kai Alhaji Dahiru Mangal ga mahaifiyarsa ba, har da sauraren bukatunta domin ya biya mata.

Yana kuma jin linzaminta yadda ya kamata. Yana tsayawa cak, inda ta tsaida shi. Ya kuma ruga inda ta aike shi. Ma’ana dai bai hada ta da komai ba. Maganarta ita ce ta karshe. Kuma ko ya takura, huskarsa ba ta nuna takurar.

 Wasu na hasashen cewa wannan ne ma sirrin nasararsa. Ta yadda yake samun nasara ga dukkan abubuwan da ya tunkara a rayuwa.

Malam Abbate wani dattijon Malami a garin Katsina wanda kuma ya rage daga cikin abokan Alhaji Bara’u wato Mahaifin Alhaji Dahiru Mangal ya bayyana mani cewa Alhaji Dahiru Mangal ya gaji wannan kyautatawa da yake yi wa Mahaifiyar tasa ne daga Kakansa Alhaji Tukur, wanda ya kan je ya gaida mahaifiyarsa, wadda ake cewa Done, a kowace rana.

Malam Abbate ya kara da cewa “Shi ma Mahaifinsa Alhaji Bara’u ya kan zo gaishe da wannan tsohuwa da kuma kawo mata abinci. Ta haka ne ma muka saba da juna, har muka zama aminan juna.

Da yake gidanta yana makwabtaka da gidanmu. Don haka, duk lokacin da ya zo ya kan shiga ya gaishe da Shehi (Mahaifinsu).”

An haifi Hajiya Murja Muhammad Dodoa shekarar 1937. Mahaifinta shi ne Alhaji Dodon Kanti.

Ita ce diyarsa ta biyu. Ta yi aure tun tana da shekara goma sha ukku (13) a duniya, a shekarar 1950.

Ta haifi ‘ya’ya takwas, hudu maza, hudu mata. Mazan su ne Alhaji Dahiru Bara’u Mangal (na farko a cikin maza, na biyu a haihuwa) da Marigayi Alhaji Muntari da Alhaji Bishir da kuma Marigayi Alhaji Marwana.

A lokacin da matan sukakasance Hajiya Hauwa (ta farko a haihuwa)da Marigayiya Hajiya Mariya da Hajiya Zulai da kuma Marigayiya Hajiya Nana Bilkisu.

Wato hudu daga cikin su ne ke raye. Biyu maza, biyu mata. Mazan su ne Alhaji Dahiru Bara’u Mangal da Alhaji Bishir Bara’uMangal.

A lokacin da matan suka kasance Hajiya Hauwa Bara’u Mangal da Hajiya Zulai Bara’u Mangal.

Hajiya Murja na daukar nauyin mutane da dama zuwa aikin Hajji da Umra, musamman ma aminanta da ‘yan’uwa da abokan arziki.

Kuma dukkan nauyi take daukewa ba tare da rage komai ga wanda ta dauki nauyinsa. Kusan dukkan tafiya-tafiyen da take yi, musamman ma aikin Hajji da umra tare take yinsu da Babbar kawarta, kuma aminiyarta ta kusa Hajiya ‘Yarbaba.

Marubucin wannan mukala ya jinjina masaa lokacin da wani abokinsa Alhaji Magaji Abdullahi Kankiya ya sheda masa cewa a lokacin da ya je aikin Hajji sun zo filin jirgiza su dawo gida a Jirgin Mad Air sai suka iske Hajiya (mahaifiyar Alhaji Dahiru Mangal) ta riga ta shiga jirgin ita ma za a dawo da ita.

Irin yadda ya ga baki dayan ma’aikatan jirgin na kazar-kazar da ~arin jikin ganin fasinjojin jirgin sun shiga jirgin a cikin gaugawa, domin kada a bata mata lokaci.

Lamarin da ya sa Alhaji Magajin ya sheda irin tsabar girmamawar da Alhaji Dahiru Mangal ke yi wa mahaifiyarsa. Wanda kuma ga shi har hakan ya yi naso ga ma’aikatansa.

Allah Ya jikanta da rahma. Ya girmama lada. Ya kuma sa Jannatul Firdausi ta zama makomarta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AttajiriBiyayyaHajiya Bara'uKatsinaMahaifiyaMangal
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalubalen Da Ke Gaban Sabon Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasa

Next Post

Muna Bukatar Tallafin Gwamnati Don Bunkasa Noma A Garin Gwanda -Mai Unguwa Yahuza

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

1 month ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Muna Bukatar Tallafin Gwamnati Don Bunkasa Noma A Garin Gwanda -Mai Unguwa Yahuza

Muna Bukatar Tallafin Gwamnati Don Bunkasa Noma A Garin Gwanda -Mai Unguwa Yahuza

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Fitar Da Fim Dake Bayyana Al’amaru Na Gaske Bisa Taken “Gajimare A Doron Kasa” 

Sin Ta Fitar Da Fim Dake Bayyana Al’amaru Na Gaske Bisa Taken “Gajimare A Doron Kasa” 

May 21, 2025
Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo

Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo

May 21, 2025
Za A Gudanar Da Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Karo Na 4 A Birnin Changsha Dake Lardin Hunan

Za A Gudanar Da Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Karo Na 4 A Birnin Changsha Dake Lardin Hunan

May 21, 2025
zulum

‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Sojoji Da ‘Yan Siyasa Wajen Samun Bayanan Sirri – Zulum 

May 21, 2025
Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

May 21, 2025
Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara

Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara

May 21, 2025
Hajjin Bana: Jihar Filato Ta Ba Da Kyautar Kujera 500 Da Tallafin Miliyan 2 Ga Duk Maniyyaci

Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77 Na Mahajjatan Nijeriya Zuwa Saudiyya 

May 21, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

‘Yansanda Sun Kama Matasa 2 Da Ake Zargi Da Satar Mota A Kebbi

May 21, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Na Ƙara Farfaɗowa – Gwamnan CBN

Tattalin Arziƙin Nijeriya Na Ƙara Farfaɗowa – Gwamnan CBN

May 21, 2025
Gwamnan Filato Ya Kafa Kwamiti Don Binciken Hare-Haren Da Ake Kai Wa A Jihar

Gwamnan Filato Ya Kafa Kwamiti Don Binciken Hare-Haren Da Ake Kai Wa A Jihar

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.