• English
  • Business News
Monday, June 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Kara Fito Da Dabarun Noman Shinkafa Ta Yadda Za A Kara Samun Riba

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Masana Sun Kara Fito Da Dabarun Noman Shinkafa Ta Yadda Za A Kara Samun Riba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin bayan ne gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani sabon tsarin noma shinkafa na kasa na shekara 10, inda masu ruwa da tsaki a a fannin suka yi amfani da damar don karfafa tsarin, yadda manoma za su ci gajiyarsa.

Wata gidauniyar bunkasa noma ta duniya da ake kira ‘Syngenta’, ta yi hadin gwiwa da shirin noma na (SFSA) don bunkasa shi yadda za a samun riba.

  • Kasar Sin Ba Ita Ce Kasar Da Ta Fi Kowacce Kasa Bayar Da Bashi Ga Kasashen Afirka Ba

Haka kuma yau, gidauniyar ta kuma yi hadaka da kamfanin Derftdan don yin nomanta yadda za a samun riba a kasar nan.
A jawabinsa a wajen taron bitar wanda aka yi a Abuja, shugaban sashin bunkasa noma Robert Berlin ya bayyana cewa, an shirya taron bitar ne domin a duba irin nasarar da aka samu a cikin shirin na SFSA, tare da samar da wani kundi don samar da gudummawa wajen karfafa aikin noma yadda za a samun riba mai yawa.

Berlin ya ce, wannan taron bitar ya zo ne bayan gwamnatin tarayya tk kaddamar da dabarun tsarin na aikin noma na kasa don samun riba ta shekaru 10,musamman domin a samar da wadatacciyarta a kasar nan, inda kuma ya yaba wa mahalarta taron kan amsa gayyatar halartar taron.

Shi ma a nasa jawabin, ministan noma da raya karkara, Dakta Mohammed Mahmood Abubakar, ya jinjina wa gidauniyar kan gagarumar gudunmawar da ta bayar don karfafa tsarin na aikin noma don samun riba.

Labarai Masu Nasaba

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

Ministan wanda Darakta a ma’aikatar, Bashir Umar ya wakilta a gurin taron ya bai wa mahalarta taron tabbacin gwamnatin tarayya don tallafa wa, musamman kananan manoman shinkafa, mussman domin a cike gibin da ake da shi na noman shinkar domin samun riba.

Abubakar ya yi kira ga mahalarta taron da su yi amfani da ilimin da suka samu a taron bitar tare da kuma wanzar da mastayar da aka cimma a gurin taron.

Shi kuwa manajan gidauniyar Isaiah Gabriel a nasa jawabin a gurin taron ya bayyana cewa, gidauniyar da kuma kamfanin Derftdan Resources ne, suka gudanar binciken domin yin nazari akan noman na shinkafar da sarrafa ta da kuma sayar da ita domin samun riba.

Gabriel ya ci gaba da cewa, nanufar mu ita ce, domin a gano kalubalen da kuma gibin da ake da shi don a karfafa tsarin na aikin noma don samun riba.

Ya sanar da cewa, ana iya Nijeriya za ta iya rungumar wannan tsarin domin a karfafa aikin noma shinkafar da kuma sarrafa ta.
A cewar Gabriel, manoma 2,249 ne suka goyi bayan gudanar da wannan binciken wanda kuma aka gudanar a jihar Koros Ribas da Neja da Edo Jigawa da Kebbi da Ebonyi da Kano da kuma Nasarawa.

Shi ma a jawabinsa a wajen taron wani babban jami’in tuntuba a fannin noma don samun riba Mista Richard Ogundele ya sanar da wasu gibin da aka samu a fannin noman shinkafa don samun riba.

A cewar Mista Richard damar da ake da ita don bunkasa noman shinkafar don samun riba, ta karade daukcin fadin kasar nan.
Ya kara da cewa, akwai bukatar a kara bunkasa noman shinkafar don samun riba a Nijeriya, musamman ga hanyar samar da kayan nomanta na yamani da samar da ingantaccen Iri.

Ya bayyana cewa, mutukar aka samar da ingancciyar shinkafar an kammala komai da ya kanata, inda ya kara da cewa, matukar aka mayar da hankali akan tsarin nomanta, hakan zai kara taimaka wa wajen nomanta a kasar nan har a kuma fitar da ita zuwa kasuwar duniya.

Mista Richard ya kara da cewa, masu ruwa da tsaki a fannin sun kuma tattauna akan matsalolin da fannin na noman shinkafar don samun riba ke fuskanta a kasar nan, inda suka bayyana cewa, akwai bukatar a yi amfani da fasahar zamani don a shawo kan matsalar, musamman domin a kara bunkasa nomanta a kasar nan.

Sauran masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun hada da, kungiyar manoman shinkafa ta kasa da cibiyar gudanar da bincike a kan amfanin gona da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Jaddada Kudirin Tallafa Wa ‘Yansanda

Next Post

Yadda Noman Karas Ke Kara Bunkasa

Related

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 days ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

1 week ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

1 week ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

2 weeks ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Yadda Noman Karas Ke Kara Bunkasa

Yadda Noman Karas Ke Kara Bunkasa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

June 15, 2025
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun Æ™i Amince Wa Da ZaÉ“en Sabon VC

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun Æ™i Amince Wa Da ZaÉ“en Sabon VC

June 15, 2025
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

June 15, 2025
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

June 15, 2025
Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

June 15, 2025
Dan Asalin Tudun Loess

Dan Asalin Tudun Loess

June 15, 2025
Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

June 15, 2025
Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

June 15, 2025
Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

June 15, 2025
APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.