ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Kara Fito Da Dabarun Noman Shinkafa Ta Yadda Za A Kara Samun Riba

by Abubakar Abba
3 years ago
Shinkafa

A kwanakin bayan ne gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani sabon tsarin noma shinkafa na kasa na shekara 10, inda masu ruwa da tsaki a a fannin suka yi amfani da damar don karfafa tsarin, yadda manoma za su ci gajiyarsa.

Wata gidauniyar bunkasa noma ta duniya da ake kira ‘Syngenta’, ta yi hadin gwiwa da shirin noma na (SFSA) don bunkasa shi yadda za a samun riba.

  • Kasar Sin Ba Ita Ce Kasar Da Ta Fi Kowacce Kasa Bayar Da Bashi Ga Kasashen Afirka Ba

Haka kuma yau, gidauniyar ta kuma yi hadaka da kamfanin Derftdan don yin nomanta yadda za a samun riba a kasar nan.
A jawabinsa a wajen taron bitar wanda aka yi a Abuja, shugaban sashin bunkasa noma Robert Berlin ya bayyana cewa, an shirya taron bitar ne domin a duba irin nasarar da aka samu a cikin shirin na SFSA, tare da samar da wani kundi don samar da gudummawa wajen karfafa aikin noma yadda za a samun riba mai yawa.

ADVERTISEMENT

Berlin ya ce, wannan taron bitar ya zo ne bayan gwamnatin tarayya tk kaddamar da dabarun tsarin na aikin noma na kasa don samun riba ta shekaru 10,musamman domin a samar da wadatacciyarta a kasar nan, inda kuma ya yaba wa mahalarta taron kan amsa gayyatar halartar taron.

Shi ma a nasa jawabin, ministan noma da raya karkara, Dakta Mohammed Mahmood Abubakar, ya jinjina wa gidauniyar kan gagarumar gudunmawar da ta bayar don karfafa tsarin na aikin noma don samun riba.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Ministan wanda Darakta a ma’aikatar, Bashir Umar ya wakilta a gurin taron ya bai wa mahalarta taron tabbacin gwamnatin tarayya don tallafa wa, musamman kananan manoman shinkafa, mussman domin a cike gibin da ake da shi na noman shinkar domin samun riba.

Abubakar ya yi kira ga mahalarta taron da su yi amfani da ilimin da suka samu a taron bitar tare da kuma wanzar da mastayar da aka cimma a gurin taron.

Shi kuwa manajan gidauniyar Isaiah Gabriel a nasa jawabin a gurin taron ya bayyana cewa, gidauniyar da kuma kamfanin Derftdan Resources ne, suka gudanar binciken domin yin nazari akan noman na shinkafar da sarrafa ta da kuma sayar da ita domin samun riba.

Gabriel ya ci gaba da cewa, nanufar mu ita ce, domin a gano kalubalen da kuma gibin da ake da shi don a karfafa tsarin na aikin noma don samun riba.

Ya sanar da cewa, ana iya Nijeriya za ta iya rungumar wannan tsarin domin a karfafa aikin noma shinkafar da kuma sarrafa ta.
A cewar Gabriel, manoma 2,249 ne suka goyi bayan gudanar da wannan binciken wanda kuma aka gudanar a jihar Koros Ribas da Neja da Edo Jigawa da Kebbi da Ebonyi da Kano da kuma Nasarawa.

Shi ma a jawabinsa a wajen taron wani babban jami’in tuntuba a fannin noma don samun riba Mista Richard Ogundele ya sanar da wasu gibin da aka samu a fannin noman shinkafa don samun riba.

A cewar Mista Richard damar da ake da ita don bunkasa noman shinkafar don samun riba, ta karade daukcin fadin kasar nan.
Ya kara da cewa, akwai bukatar a kara bunkasa noman shinkafar don samun riba a Nijeriya, musamman ga hanyar samar da kayan nomanta na yamani da samar da ingantaccen Iri.

Ya bayyana cewa, mutukar aka samar da ingancciyar shinkafar an kammala komai da ya kanata, inda ya kara da cewa, matukar aka mayar da hankali akan tsarin nomanta, hakan zai kara taimaka wa wajen nomanta a kasar nan har a kuma fitar da ita zuwa kasuwar duniya.

Mista Richard ya kara da cewa, masu ruwa da tsaki a fannin sun kuma tattauna akan matsalolin da fannin na noman shinkafar don samun riba ke fuskanta a kasar nan, inda suka bayyana cewa, akwai bukatar a yi amfani da fasahar zamani don a shawo kan matsalar, musamman domin a kara bunkasa nomanta a kasar nan.

Sauran masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun hada da, kungiyar manoman shinkafa ta kasa da cibiyar gudanar da bincike a kan amfanin gona da sauransu.

Shinkafa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Yadda Noman Karas Ke Kara Bunkasa

Yadda Noman Karas Ke Kara Bunkasa

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.