ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Baje Koli 1,000 Za Su Baje Hajarsu A Kasuwar Duniya Ta Jihar Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
3 weeks ago
Baje koli

Rukunonin Kamfanin Dangote ya sanar da cewa, zai shiga Kasuwar Baje Koli ta kasa da kasa da za a gudanar a jihar Kano.

An tsara za a bude kasuwar baje kolin ne, daga ranar 22 na watan Nuwamba zuwa ranar 6 ga watan Disambar shekarar 2025, inda ake sa ran, sama kamfanonin a cikin kasar nan da kuma na waje 1000, za su baje kolin hajarsu.

  • Tawagar Atiku Ta Isa Bauchi Don Halartar Jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

Babban Shugaban Sashen Samar da Bayanai na Kamfanin Anthony Chiejina, ne ya sanar da hakan.

ADVERTISEMENT

Anthony ya sanar da cewa, Kamfanin na Dangote ne, zai dauki nauyin gudanar da baje kolin tare da kuma shiga cikin baje kolin gadan-gadan.

Ya kara da cewa, ana sa ran sama da masu baje kolin daga cikin kasar da kuma ketare, za su baje hajarsu, a kasuwar.

LABARAI MASU NASABA

Danyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.436 —OPEC

An Jinjina Wa Tinubu Bisa Mayar Da Ofishin Ayyukan NPA Garin Warri

“Jihar Kano, ta kasance tamkar cibiyar hada-hadar kasuwanci, ba wai a kawai a Nijeriya ba, har da ma a nahiyar Afirka,” in ji Anthony.

Ya ci gaba da cewa, kamfanin ya kuma kasance ya na da manyan kamfanonin da ke tsasar Shinka, a jihar ta Kano.

Kazalika, ya sanar da cewa, kamfanin na da kuma wasu kamfanonin tsadar Shinkafa da a jihohin Jigawa, Zamfara, Nijer, Kebbi, da kuma Sokoto, wanada ke da karfin tsasar Shinkfar da ta kai jimlra tan miliyan 1.5 a duk shekara.

Ya bayyana cewa, kamfanin yayi hakan ne, musamman bisa nufin tallafa wa kokarin gawamnati na samar da wadataccen abinci a kasar baki daya.

A cewarsa, kamfanin zai tabbatar da cewa, sauran sassansa sun taimaka wajen ganin an samu cin nasara, na gudanar da baje kolin a cikin nasara, tare da kuma bai wa masu yin kasuwancin kwarin guiwa wajen yin hadaka da kamfanin na Dangote.

Ya sanar da cewa, duba da matukar bukatar da ake da ita a kasuwani na Suga, kamfanin zai yin amfani da damar ta baje kolin wajen yin baje kolin sabon buhun samfarin Suga, mai nauyin daga kilo 100 da kuma kilo 25.

Ya sanar da cewa, taken baje kolin na bana, wanda shi ne, karfafa kwarin guiwar kanana da matsakaitan sana’oi, taken ya zo daidai da manufar kamfanin na Dangote, na tallafa wa kanana da matsakaitan sana’oi a kasar.

Ita kuwa, Babbar Mai Bai Wa Shugaban Rukunonin Kamfanin na Dangote Alhaji Aliko Dangote Shawar ta Musamman a bangaren Gudanar da Ayyuka da Dabaru da kuma Hulda da Jama’a Fatima Wali-Abdurrahman a cikin sanarwar da ta fitar ta ce, bisa daukar nauyin gudanar da baje kolin na bana, Kamfanin zai tabbatar da ya karfafa kwarin guiwar kanana da matsakaitan sana’oi, wanda hakan, zai basu damar baje hajar su, a lokacin baje kolin.

Shi kuwa Shugaban Cibiyar Kasuwar Baje Kolin Masana’antu da Ma’adanai da Aikin Noma KACCIMA Jakada Hassan Usman Darma, ya sanar da cewa, “ Muna sa ran kamfanonin kimanin 100 da kuma wasu masu baje kolin sama da 1,000, daga ciki da wajen kasar, za su baje hajaarsu, a kasuwar.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Danyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.436 —OPEC
Tattalin Arziki

Danyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.436 —OPEC

December 19, 2025
An Jinjina Wa Tinubu Bisa Mayar Da Ofishin Ayyukan NPA Garin Warri
Tattalin Arziki

An Jinjina Wa Tinubu Bisa Mayar Da Ofishin Ayyukan NPA Garin Warri

December 19, 2025
Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji
Tattalin Arziki

Gwamna Radda Ya Dora Harsashin Gina Ma’aikatar Sarrafa Rogo A Katsina

December 13, 2025
Next Post
Sabuwar Manufar Habaka Ciniki Ta Sin Ta Samarwa Duniya Manyan Damammaki

Sabuwar Manufar Habaka Ciniki Ta Sin Ta Samarwa Duniya Manyan Damammaki

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.