ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Baje Koli 1,000 Za Su Baje Hajarsu A Kasuwar Duniya Ta Jihar Kano

by Abubakar Abba and Sulaiman
9 months ago
Baje koli

Rukunonin Kamfanin Dangote ya sanar da cewa, zai shiga Kasuwar Baje Koli ta kasa da kasa da za a gudanar a jihar Kano.

An tsara za a bude kasuwar baje kolin ne, daga ranar 22 na watan Nuwamba zuwa ranar 6 ga watan Disambar shekarar 2025, inda ake sa ran, sama kamfanonin a cikin kasar nan da kuma na waje 1000, za su baje kolin hajarsu.

  • Tawagar Atiku Ta Isa Bauchi Don Halartar Jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

Babban Shugaban Sashen Samar da Bayanai na Kamfanin Anthony Chiejina, ne ya sanar da hakan.

ADVERTISEMENT

Anthony ya sanar da cewa, Kamfanin na Dangote ne, zai dauki nauyin gudanar da baje kolin tare da kuma shiga cikin baje kolin gadan-gadan.

Ya kara da cewa, ana sa ran sama da masu baje kolin daga cikin kasar da kuma ketare, za su baje hajarsu, a kasuwar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

“Jihar Kano, ta kasance tamkar cibiyar hada-hadar kasuwanci, ba wai a kawai a Nijeriya ba, har da ma a nahiyar Afirka,” in ji Anthony.

Ya ci gaba da cewa, kamfanin ya kuma kasance ya na da manyan kamfanonin da ke tsasar Shinka, a jihar ta Kano.

Kazalika, ya sanar da cewa, kamfanin na da kuma wasu kamfanonin tsadar Shinkafa da a jihohin Jigawa, Zamfara, Nijer, Kebbi, da kuma Sokoto, wanada ke da karfin tsasar Shinkfar da ta kai jimlra tan miliyan 1.5 a duk shekara.

Ya bayyana cewa, kamfanin yayi hakan ne, musamman bisa nufin tallafa wa kokarin gawamnati na samar da wadataccen abinci a kasar baki daya.

A cewarsa, kamfanin zai tabbatar da cewa, sauran sassansa sun taimaka wajen ganin an samu cin nasara, na gudanar da baje kolin a cikin nasara, tare da kuma bai wa masu yin kasuwancin kwarin guiwa wajen yin hadaka da kamfanin na Dangote.

Ya sanar da cewa, duba da matukar bukatar da ake da ita a kasuwani na Suga, kamfanin zai yin amfani da damar ta baje kolin wajen yin baje kolin sabon buhun samfarin Suga, mai nauyin daga kilo 100 da kuma kilo 25.

Ya sanar da cewa, taken baje kolin na bana, wanda shi ne, karfafa kwarin guiwar kanana da matsakaitan sana’oi, taken ya zo daidai da manufar kamfanin na Dangote, na tallafa wa kanana da matsakaitan sana’oi a kasar.

Ita kuwa, Babbar Mai Bai Wa Shugaban Rukunonin Kamfanin na Dangote Alhaji Aliko Dangote Shawar ta Musamman a bangaren Gudanar da Ayyuka da Dabaru da kuma Hulda da Jama’a Fatima Wali-Abdurrahman a cikin sanarwar da ta fitar ta ce, bisa daukar nauyin gudanar da baje kolin na bana, Kamfanin zai tabbatar da ya karfafa kwarin guiwar kanana da matsakaitan sana’oi, wanda hakan, zai basu damar baje hajar su, a lokacin baje kolin.

Shi kuwa Shugaban Cibiyar Kasuwar Baje Kolin Masana’antu da Ma’adanai da Aikin Noma KACCIMA Jakada Hassan Usman Darma, ya sanar da cewa, “ Muna sa ran kamfanonin kimanin 100 da kuma wasu masu baje kolin sama da 1,000, daga ciki da wajen kasar, za su baje hajaarsu, a kasuwar.”

Baje koli
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Baje koli
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
Sabuwar Manufar Habaka Ciniki Ta Sin Ta Samarwa Duniya Manyan Damammaki

Sabuwar Manufar Habaka Ciniki Ta Sin Ta Samarwa Duniya Manyan Damammaki

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.