ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing

by Sulaiman
52 minutes ago

A jiya Talata ne mataimakin shugaban kasar Sin Han Zheng ya gabatar da jawabi, a liyafar da aka shirya don nuna maraba da baki mahalarta taron dandalin tattaunawa na Xiangshan da ake gudanarwa kan sha’anin tsaro a birnin Beijing karo na 13, inda wakilai daga kasashe da yankuna da kuma kungiyoyin duniya kusan 100 suka halarta. 

A jawabin da ya gabtar, ya ce duk da kalubalen da duniya ke fuskanta a halin yanzu, manufar samar da zaman lafiya, bunkasa ci gaba, hadin gwiwar kasashe, da samun nasara ga kowane bangare, abu ne da ba za a iya dakatar da shi ba, sannan babu ja da baya kan yanayin da ake ciki na samun bunkasar kasashe daban daban da dunkulewar tattalin arzikin duniya wuri guda. 

Han Zheng ya jaddada bukatar kiyaye manufofi da dokokin MDD, da tsayawa kan ingantaccen tsarin hadin gwiwar kasa da kasa, warware rikice-rikice ta hanyar tattaunawa da tuntubar juna, sanya bukatar al’umma a gaba da kome, da kuma tabbatar da cewa fasahohi sun zama abin moriya ga cigaban dan Adam. 

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa a a matsayin Sin na babbar kasa kuma kasa mai tasowa mafi girma a duniya, a kullum tana sanya ci gabanta ne domin bunkasa rayuwar dan Adam, da kuma ba da gudunmawarta domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya, da kuma ci gaba ta hanyar zamanantar da kanta. 

Har ila yau, yayin da ake bikin bude taron dandalin Xiangshan na Beijing karo na 13 a yau Laraba, minitan tsaron kasar Sin, Dong Jun ya jaddada batun kiyaye kwanciyar hankali a bisa tsarin mabambantan bangarori. Dong ya yi kira da a ci gaba da yin riko da tsarin mabambantan bangarori na hakika, da kafe kai da fata wajen kiyaye tsarin kasa da kasa a karkashin MDD, da kuma tsarin duniya da aka shimfida bisa dokokin kasa da kasa. 

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin

Kazalika, Dong ya jaddada bukatar sanya darussan da aka koya daga tarihi a cikin zukata da ci gaba da sa-ido sosai game da babakeren wata kasa, da tara karfin soji da kuma maimaita tarihi. Dong ya yi nuni da cewa, darussa masu daci da aka koya daga yake-yaken duniya da bala’o’in rikice-rikice da hargitsin da ake fama da su a yau, suna gargadi ne kan cewa rigakafin barkewar rikici dabara ce mafi muhimmanci a bangaren tafiyar da sha’anin tsaro.  

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa
  • Sulaiman
    Haɓaka Tattalin Arzikin Zamfara: Gwamna Lawal Zai Halarci Babban Taron MDD A New York
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Hallaka Wani Jagoran ’Yan Ta’adda A Katsina
  • Sulaiman
    Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin

MASU ALAKA

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

September 16, 2026
Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin

September 16, 2026
Hanyar Ruwa Ta pinglu Ta Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN
Daga Birnin Sin

Hanyar Ruwa Ta pinglu Ta Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN

September 16, 2026
Next Post
Haɓaka Tattalin Arzikin Zamfara: Gwamna Lawal Zai Halarci Babban Taron MDD A New York

Haɓaka Tattalin Arzikin Zamfara: Gwamna Lawal Zai Halarci Babban Taron MDD A New York

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

Nazarin CGTN: Dole Ne Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Samar Da Tsaro Mai Dorewa

September 16, 2026
Haɓaka Tattalin Arzikin Zamfara: Gwamna Lawal Zai Halarci Babban Taron MDD A New York

Haɓaka Tattalin Arzikin Zamfara: Gwamna Lawal Zai Halarci Babban Taron MDD A New York

September 16, 2026
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Dandalin Xiangshan Da Ake Gudanarwa Kan Sha’anin Tsaro A Beijing

September 16, 2026
Wani Mai Taɓin Ƙwaƙwalwa Ya Kashe Soja A Legas

Sojoji Sun Hallaka Wani Jagoran ’Yan Ta’adda A Katsina

September 16, 2026
Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin

Lee Ka Chiu: Shirin Shekaru 5 Na Farko Na Raya Yankin Musamman Na Hong Kong Ya Dace Da Muradun Kasar Sin

September 16, 2026
Gwamnatinmu Za Ta Kawar Da Talauci Da Zarar An Zabe Mu – Shettima

Gwamnonin Arewa 6 Kacal Ne Suka Goyi Bayan Tinubu A 2023 – Shettima

September 16, 2026
Hanyar Ruwa Ta pinglu Ta Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN

Hanyar Ruwa Ta pinglu Ta Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN

September 16, 2026
peter

Peter Obi Ya Nemi ‘Yan Nijeriya Su Sayi Hannun Jarin Matatar Mai Ta Dangote

September 16, 2026
Manufar Sin Kan Raba Fasahar AI Ga Saura: Hakika Mai Bayarwa Ba Ya Rasawa

Manufar Sin Kan Raba Fasahar AI Ga Saura: Hakika Mai Bayarwa Ba Ya Rasawa

September 16, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 240 Bisa Zargin Laifuka Daban-Daban A Yobe

September 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.