Mataimakin Shugaban Kasa,, Kashim Shettima, ya bayyana cewa gwamnonin jihohin Arewa shida kacal daga cikin 19 ne suka goyi bayan takarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na 2023.
Shettima ya bayyana hakan ne ranar Laraba a fadar Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, yayin bikin naɗa Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, sarautar Sardaunan Masarautar Ilorin.
Ya ce yanayin siyasar da ya dabaibaye zaɓen shugaban ƙasa na 2023 ya kasance mai tsauri, inda aka fuskanci kalubale da dama a kan tafiyar Tinubu, amma hakan bai hana shi ci gaba da neman shugabancin ƙasar ba.
Mataimakin shugaban ƙasar ya ce wannan ƙwarewa ya kamata ta zama darasi ga ’yan siyasar da ke shirin shiga zaɓuka a nan gaba.
Ya jaddada cewa bambance-bambancen siyasa bai kamata ya haifar da rarrabuwar kawuna na dindindin tsakanin ’yan siyasar da ke neman mukaman zaɓe ba.
Shettima ya kuma yi kira ga ’yan siyasar Jihar Kwara da su sasanta tsakaninsu bayan kammala zaɓen fidda gwani na APC, ba tare da la’akari da wanda ya yi nasara ba.













