Dakarun haɗin gwiwar rundunar tsaron Arewa maso Yamma, Operation FANSAN YAMMA, sun hallaka wasu ’yan ta’adda biyu, ciki har da wani fitaccen shugaban ’yan ta’adda mai suna Abbah Alhassan, tare da kama wasu mutane biyu da ake zargin ’yan ta’adda ne a wasu samame daban-daban a Jihar Katsina.
Ayyukan sun gudana ne a ranar 15 ga Satumba, 2026, bayan dakarun Sector 2 sun samu sahihan bayanan sirri cewa ’yan ta’addan na shirin kai hare-hare kan wasu al’ummomi a ƙananan hukumomin Matazu da Kankara.
Bayan samun bayanan, sojojin sun nufi maɓoyar ’yan ta’addan, inda suka yi musayar wuta da su. An hallaka ’yan ta’adda biyu, ciki har da Abbah Alhassan, yayin da sauran suka tsere zuwa cikin daji.
Rundunar ta ce ayyukan na daga cikin matakan da take ɗauka domin dakile hare-haren ’yan ta’adda da kuma ƙarfafa tsaro a yankunan Arewa maso Yamma.














