Rundunar ’Yansandan Jihar Yobe ta kama mutane 240 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban, ciki har da kisan kai, fyade, garkuwa da mutane da fashi da makami, cikin watanni uku da suka gabata.
Kwamishinan ’Yansandan jihar, Usman Jibrin, ne ya bayyana hakan ranar Laraba yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Damaturu.
Ya ce kamen ya biyo bayan binciken wasu kararrakin kisan kai 16, fyade 9, garkuwa da mutum guda, kararrakin karɓar kuɗi ta hanyar barazana guda biyu, fashi da makami biyar, da kuma wasu laifuka daban-daban 112 da aka samu tsakanin watan Yuli zuwa Satumba.
Kwamishinan ya ce rundunar ta samu gagarumin ci gaba wajen yaƙi da aikata laifuka a jihar a tsawon wannan lokaci.
Ya ce: “Mun samu gagarumin ci gaba wajen yaƙi miyagun ayyuka a jihar. A cikin lokacin da ake nazari, mun kama mutane 240 bisa zargin aikata laifuka daban-daban.”














