• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Yayata Ilimin Kimiya Na Kasar Sin Zai Amfani Duniya Baki Daya

by CMG Hausa
3 years ago
Kimiya

A kwanakin baya ne mahukuntan kasar Sin, suka fitar da wani kundin bayani, mai kunshe da matakan yayata ilimin kimiyya tsakanin al’ummar kasar, matakan da ake fatan za su taimaka wajen ingiza kwazon al’umma a fannin samar da ci gaba ta hanyar yin kirkire-kirkire.

Ofisoshin sakatariyar kwamitin tsakiya na JKS, da majalisar gudanarwar kasar ne suka fitar da kundin cikin hadin gwiwa. Kundin ya kuma karfafa muhimmancin hade matakan yayata ilimin kimiyya, da fannin kirkire kirkiren kimiyya da fasaha.

  • Kasashe Da Dama Na Sa Ran Habaka Kasuwannin Cinikayyar Hidimomin Kasar Sin Ta Hanyar Halartar Bikin CIFTIS

Kana ya fayyace sassa daban daban game da irin matakan da za a aiwatar domin cimma nasarar da aka sanya gaba.

An tsara cewa, ya zuwa shekarar 2025, za a kai ga fafada ayyukan yayata ilimin kimiyya tsakanin al’umma, inda masu bincike za su kara taka muhimmiyar rawa, wajen yada ilimin kimiyya, ana kuma sa ran adadin al’ummar kasar Sin masana ilimin kimiyya zai haura kashi 15 bisa 100, kana adadin ’yan kasar masu maida hankali ga kimiyya da kirkire-kirkire zai yi matukar karuwa.

Kundin ya kara zayyana cewa, ya zuwa shekarar 2035, ana sa ran adadin al’ummar kasar Sin masu sani game da ilimin kimiyya zai kai kashi 25 bisa dari, yayin da yawaitar masu fahimtar kimiyya zai taka muhimmiyar rawa wajen samar da ingantaccen ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Abin da ke kara bayyana cewa, kimiya da fasahar kirkire-kirkire sun kasance muhimman tushen ci gaban kasa a wannan zamani.

Wannan na zuwa ne, yayin da aka yi nasarar kammala bikin baje kolin cinikayyar hidima na kasa da kasa na kasar Sin na wannan shekara.

Yayin bikin na kwanaki 6, an gudanar da jigon taruka sama da 100 da gabatarwa da shawarwari fiye da 60, wanda ya cimma jimillar nau’o’in sakamako 1,333 da suka hada da hada-hadar kasuwanci, da saka jari, da gabatar da dabaru da yarjeniyoyin hannayen jarin kirkire-kirkire a sauransu. A bana yawan mahalarta taron ya zarce dubu 250.

Sabanin yadda a mafi yawan lokuta irin wadannan bukukuwan baje koli ke karewa a matsayin wani taro na shan-shayi, bikin CIFTIS na bana, ya zama mafi girma a bangaren ma’auni da kimar bunkasa duniya.

Ya kuma janyo hankalin manyan kamfanoni 507 dake sahun gaba a duniya, inda suka halarci bikin a zahiri.
A karon farko an gabatarwa kamfanoni da cibiyoyi sabbin samfuran fiye da 100 da sabbin fasahohi na nasarori a fannonin kwaikwayoyin tunanin dan-Adam.

Duk da cikas din da ake fuskanta a kokarin da ake na dunkulewar duniya gami da rikice-rikice da ake fuskanta a sassan duniya, bikin na CIFTIS ya kara samun mahalarta, saboda wasu muhimman dalilai, da suka hada da yadda kasuwar kasar Sin take jawo hankali sosai, da yadda bikin ya zama muhimmiyar alamar yadda kasar Sin take kara bude kofa ga kasashen ketare, zurfafa hadin gwiwa, da ba da jagora kan yin kirkire-kirkire, da nuna aniyar kasar Sin ta kara azama kan dinkewar tattalin arzikin duniya, lamarin da kasashen duniya ke matukar bukata yanzu. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
Next Post
Saudiyya Ta Ja Kunnen Netflix Kan Yada Fina-Finan Da Suka Keta Dokokin Musulunci

Saudiyya Ta Ja Kunnen Netflix Kan Yada Fina-Finan Da Suka Keta Dokokin Musulunci

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.