• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Yayata Ilimin Kimiya Na Kasar Sin Zai Amfani Duniya Baki Daya

by CMG Hausa
3 years ago
Kimiya

A kwanakin baya ne mahukuntan kasar Sin, suka fitar da wani kundin bayani, mai kunshe da matakan yayata ilimin kimiyya tsakanin al’ummar kasar, matakan da ake fatan za su taimaka wajen ingiza kwazon al’umma a fannin samar da ci gaba ta hanyar yin kirkire-kirkire.

Ofisoshin sakatariyar kwamitin tsakiya na JKS, da majalisar gudanarwar kasar ne suka fitar da kundin cikin hadin gwiwa. Kundin ya kuma karfafa muhimmancin hade matakan yayata ilimin kimiyya, da fannin kirkire kirkiren kimiyya da fasaha.

  • Kasashe Da Dama Na Sa Ran Habaka Kasuwannin Cinikayyar Hidimomin Kasar Sin Ta Hanyar Halartar Bikin CIFTIS

Kana ya fayyace sassa daban daban game da irin matakan da za a aiwatar domin cimma nasarar da aka sanya gaba.

An tsara cewa, ya zuwa shekarar 2025, za a kai ga fafada ayyukan yayata ilimin kimiyya tsakanin al’umma, inda masu bincike za su kara taka muhimmiyar rawa, wajen yada ilimin kimiyya, ana kuma sa ran adadin al’ummar kasar Sin masana ilimin kimiyya zai haura kashi 15 bisa 100, kana adadin ’yan kasar masu maida hankali ga kimiyya da kirkire-kirkire zai yi matukar karuwa.

Kundin ya kara zayyana cewa, ya zuwa shekarar 2035, ana sa ran adadin al’ummar kasar Sin masu sani game da ilimin kimiyya zai kai kashi 25 bisa dari, yayin da yawaitar masu fahimtar kimiyya zai taka muhimmiyar rawa wajen samar da ingantaccen ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Abin da ke kara bayyana cewa, kimiya da fasahar kirkire-kirkire sun kasance muhimman tushen ci gaban kasa a wannan zamani.

Wannan na zuwa ne, yayin da aka yi nasarar kammala bikin baje kolin cinikayyar hidima na kasa da kasa na kasar Sin na wannan shekara.

Yayin bikin na kwanaki 6, an gudanar da jigon taruka sama da 100 da gabatarwa da shawarwari fiye da 60, wanda ya cimma jimillar nau’o’in sakamako 1,333 da suka hada da hada-hadar kasuwanci, da saka jari, da gabatar da dabaru da yarjeniyoyin hannayen jarin kirkire-kirkire a sauransu. A bana yawan mahalarta taron ya zarce dubu 250.

Sabanin yadda a mafi yawan lokuta irin wadannan bukukuwan baje koli ke karewa a matsayin wani taro na shan-shayi, bikin CIFTIS na bana, ya zama mafi girma a bangaren ma’auni da kimar bunkasa duniya.

Ya kuma janyo hankalin manyan kamfanoni 507 dake sahun gaba a duniya, inda suka halarci bikin a zahiri.
A karon farko an gabatarwa kamfanoni da cibiyoyi sabbin samfuran fiye da 100 da sabbin fasahohi na nasarori a fannonin kwaikwayoyin tunanin dan-Adam.

Duk da cikas din da ake fuskanta a kokarin da ake na dunkulewar duniya gami da rikice-rikice da ake fuskanta a sassan duniya, bikin na CIFTIS ya kara samun mahalarta, saboda wasu muhimman dalilai, da suka hada da yadda kasuwar kasar Sin take jawo hankali sosai, da yadda bikin ya zama muhimmiyar alamar yadda kasar Sin take kara bude kofa ga kasashen ketare, zurfafa hadin gwiwa, da ba da jagora kan yin kirkire-kirkire, da nuna aniyar kasar Sin ta kara azama kan dinkewar tattalin arzikin duniya, lamarin da kasashen duniya ke matukar bukata yanzu. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

October 24, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Next Post
Saudiyya Ta Ja Kunnen Netflix Kan Yada Fina-Finan Da Suka Keta Dokokin Musulunci

Saudiyya Ta Ja Kunnen Netflix Kan Yada Fina-Finan Da Suka Keta Dokokin Musulunci

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

October 24, 2025
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025, Injiniya Abdullahi Sule

October 24, 2025
Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

October 24, 2025

Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Sheriff Oboreɓwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

October 24, 2025
An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

October 24, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.