ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Yayata Ilimin Kimiya Na Kasar Sin Zai Amfani Duniya Baki Daya

by CMG Hausa
4 years ago
Kimiya

A kwanakin baya ne mahukuntan kasar Sin, suka fitar da wani kundin bayani, mai kunshe da matakan yayata ilimin kimiyya tsakanin al’ummar kasar, matakan da ake fatan za su taimaka wajen ingiza kwazon al’umma a fannin samar da ci gaba ta hanyar yin kirkire-kirkire.

Ofisoshin sakatariyar kwamitin tsakiya na JKS, da majalisar gudanarwar kasar ne suka fitar da kundin cikin hadin gwiwa. Kundin ya kuma karfafa muhimmancin hade matakan yayata ilimin kimiyya, da fannin kirkire kirkiren kimiyya da fasaha.

  • Kasashe Da Dama Na Sa Ran Habaka Kasuwannin Cinikayyar Hidimomin Kasar Sin Ta Hanyar Halartar Bikin CIFTIS

Kana ya fayyace sassa daban daban game da irin matakan da za a aiwatar domin cimma nasarar da aka sanya gaba.

ADVERTISEMENT

An tsara cewa, ya zuwa shekarar 2025, za a kai ga fafada ayyukan yayata ilimin kimiyya tsakanin al’umma, inda masu bincike za su kara taka muhimmiyar rawa, wajen yada ilimin kimiyya, ana kuma sa ran adadin al’ummar kasar Sin masana ilimin kimiyya zai haura kashi 15 bisa 100, kana adadin ’yan kasar masu maida hankali ga kimiyya da kirkire-kirkire zai yi matukar karuwa.

Kundin ya kara zayyana cewa, ya zuwa shekarar 2035, ana sa ran adadin al’ummar kasar Sin masu sani game da ilimin kimiyya zai kai kashi 25 bisa dari, yayin da yawaitar masu fahimtar kimiyya zai taka muhimmiyar rawa wajen samar da ingantaccen ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Abin da ke kara bayyana cewa, kimiya da fasahar kirkire-kirkire sun kasance muhimman tushen ci gaban kasa a wannan zamani.

Wannan na zuwa ne, yayin da aka yi nasarar kammala bikin baje kolin cinikayyar hidima na kasa da kasa na kasar Sin na wannan shekara.

Yayin bikin na kwanaki 6, an gudanar da jigon taruka sama da 100 da gabatarwa da shawarwari fiye da 60, wanda ya cimma jimillar nau’o’in sakamako 1,333 da suka hada da hada-hadar kasuwanci, da saka jari, da gabatar da dabaru da yarjeniyoyin hannayen jarin kirkire-kirkire a sauransu. A bana yawan mahalarta taron ya zarce dubu 250.

Sabanin yadda a mafi yawan lokuta irin wadannan bukukuwan baje koli ke karewa a matsayin wani taro na shan-shayi, bikin CIFTIS na bana, ya zama mafi girma a bangaren ma’auni da kimar bunkasa duniya.

Ya kuma janyo hankalin manyan kamfanoni 507 dake sahun gaba a duniya, inda suka halarci bikin a zahiri.
A karon farko an gabatarwa kamfanoni da cibiyoyi sabbin samfuran fiye da 100 da sabbin fasahohi na nasarori a fannonin kwaikwayoyin tunanin dan-Adam.

Duk da cikas din da ake fuskanta a kokarin da ake na dunkulewar duniya gami da rikice-rikice da ake fuskanta a sassan duniya, bikin na CIFTIS ya kara samun mahalarta, saboda wasu muhimman dalilai, da suka hada da yadda kasuwar kasar Sin take jawo hankali sosai, da yadda bikin ya zama muhimmiyar alamar yadda kasar Sin take kara bude kofa ga kasashen ketare, zurfafa hadin gwiwa, da ba da jagora kan yin kirkire-kirkire, da nuna aniyar kasar Sin ta kara azama kan dinkewar tattalin arzikin duniya, lamarin da kasashen duniya ke matukar bukata yanzu. (Ibrahim Yaya)

Kimiya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Saudiyya Ta Ja Kunnen Netflix Kan Yada Fina-Finan Da Suka Keta Dokokin Musulunci

Saudiyya Ta Ja Kunnen Netflix Kan Yada Fina-Finan Da Suka Keta Dokokin Musulunci

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.