ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matashi Zai Biya Diyyar Miliyan 52 Saboda Yi Wa Wani Rauni A Kano

by Sadiq
3 years ago
Diyya

Wata kotun shari’ar Muslunci da ke zamanta a unguwar PRP a jihar Kano ta yanke wa wani matashi mai suna Abubakar Ayuba, mai shekaru 20 a duniya da ta samu da laifin yi wa wani Salisu Usaini mummunan rauni a hannu, har ta kai ga hannun ya rube aka yanke shi a asibiti, hukuncin biyan diyyar miliyan 52.

Laifin, a cewar alkalin kotun, Nura Yusuf Ahmad, ya sabawa sashe na 159 na kundin dokar laifuka (Penal Code) ta jihar Kano.

  • Babu Wata Shawara Da DSS Ta Aike Wa Buhari Kan Takarar Musulmi Da Musulmi – Fadar Shugaban Kasa
  • Rufe Iyakoki Ya Yi Amfani Saboda Mutane Na Cin Shinkafar Gida Yanzu – Buhari

Shi ya sa alkali Ahmad ya yanke wa mai laifin hukuncin daurin watanni shida a gidan yari da kuma biyan diyyar Naira Miliyan 52 da dubu 970 a cikin shekaru ga mai karar.

ADVERTISEMENT

Alkalin ya kuma umarci wanda a ke karar da ya biya Naira dubu 650 kudin magani ga wanda ya shigar da kara ya yi tun daga farkon jin raunin har zuwa warkewarsa.

Tun da fari dai, a ranar 20 ga watan Maris, 2022 aka zargi Abubakar da daukar wata sharbebiyar wuka ya kuma kaftawa matashi Salisu Usaini a hannunsa na dama, kuma a dalilin wannan aika-aikar ne ya janyo likitoci suka tabbatar da cewar babu shakka sai dai a guntule hannun, saboda tuni hannun ya rube.

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Amarya Da Hallaka Mijinta Har Lahira A Katsina

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

Koda likitoci suka cire hannun matashin, sai fa hannu ya ci gaba da rubewa har sai da hakan ya sanya aka sake yi masa aiki, daga karshe kuma sai da aka guntile hannun gaba daya tun daga allon kafadarsa.

Da aka kai mai laifin kotu, mai gabatar da kara, Aliyu Zainul Abideen ne ya karanta wa matashin tuhumar da aike yi masa, tun kuma a wancan lokaci Abubakar ya amsa wannan zargi da a ke yi masa.

Hakan ne ya sanya kotun ta umarci jami’an gidan gyaran hali da su ajiye shi har sai anga yanayin halin da mara lafiyar yake ciki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ana Zargin Amarya Da Hallaka Mijinta Har Lahira A Katsina
Al'ajabi

Ana Zargin Amarya Da Hallaka Mijinta Har Lahira A Katsina

November 25, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Next Post
Kashu

Noman Kashu A Saukake

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.