ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matashi Zai Biya Diyyar Miliyan 52 Saboda Yi Wa Wani Rauni A Kano

by Sadiq
4 years ago
Diyya

Wata kotun shari’ar Muslunci da ke zamanta a unguwar PRP a jihar Kano ta yanke wa wani matashi mai suna Abubakar Ayuba, mai shekaru 20 a duniya da ta samu da laifin yi wa wani Salisu Usaini mummunan rauni a hannu, har ta kai ga hannun ya rube aka yanke shi a asibiti, hukuncin biyan diyyar miliyan 52.

Laifin, a cewar alkalin kotun, Nura Yusuf Ahmad, ya sabawa sashe na 159 na kundin dokar laifuka (Penal Code) ta jihar Kano.

  • Babu Wata Shawara Da DSS Ta Aike Wa Buhari Kan Takarar Musulmi Da Musulmi – Fadar Shugaban Kasa
  • Rufe Iyakoki Ya Yi Amfani Saboda Mutane Na Cin Shinkafar Gida Yanzu – Buhari

Shi ya sa alkali Ahmad ya yanke wa mai laifin hukuncin daurin watanni shida a gidan yari da kuma biyan diyyar Naira Miliyan 52 da dubu 970 a cikin shekaru ga mai karar.

ADVERTISEMENT

Alkalin ya kuma umarci wanda a ke karar da ya biya Naira dubu 650 kudin magani ga wanda ya shigar da kara ya yi tun daga farkon jin raunin har zuwa warkewarsa.

Tun da fari dai, a ranar 20 ga watan Maris, 2022 aka zargi Abubakar da daukar wata sharbebiyar wuka ya kuma kaftawa matashi Salisu Usaini a hannunsa na dama, kuma a dalilin wannan aika-aikar ne ya janyo likitoci suka tabbatar da cewar babu shakka sai dai a guntule hannun, saboda tuni hannun ya rube.

LABARAI MASU NASABA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

Koda likitoci suka cire hannun matashin, sai fa hannu ya ci gaba da rubewa har sai da hakan ya sanya aka sake yi masa aiki, daga karshe kuma sai da aka guntile hannun gaba daya tun daga allon kafadarsa.

Da aka kai mai laifin kotu, mai gabatar da kara, Aliyu Zainul Abideen ne ya karanta wa matashin tuhumar da aike yi masa, tun kuma a wancan lokaci Abubakar ya amsa wannan zargi da a ke yi masa.

Hakan ne ya sanya kotun ta umarci jami’an gidan gyaran hali da su ajiye shi har sai anga yanayin halin da mara lafiyar yake ciki.

MASU ALAKA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Al'ajabi

Ɓata-gari Sun Kashe Matar Aure Da ’Ya’yanta 3 A Kano

January 21, 2026
Next Post
Kashu

Noman Kashu A Saukake

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.