• English
  • Business News
Thursday, August 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matashin Da Ya Kware Wajen Satar Na’urorin AC A Kotu, Ya Fada Komar ‘Yansanda

by Abubakar Abba
10 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani matashi dan shekara 20, mai suna Mohammed Sani da ake zargin ya kware wajen sace-sacen na’urorin sanyaya dakuna wato AC a kotuna jihar, ya fada a komar rundunar ‘yansandan Jihar Kaduna.

A yayin da kakakin rundunar ‘yansandan jihar ASP Mansur Hassan ya bajen kolin Sani a gaban ‘yan jairida, Sani ya shedawa ‘yan jaridar cewa, ya kware wajen satar na’urorin a kutuna da kuma na wasu ofis-ofis na gwamnatin jihar.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • Sin Ta Shirya Daukar Baje Kolin CIIE A Matsayin Wata Dama Ta Gabatar Da Damarmakin Babbar Kasuwarta Ga Duniya

Yaron ya yi ikirarin cewa, wani uban gidansa ne mai suna Isma’il, ke tura shi yin satar ta hanyar bashi wata takarda da ke nuna cewa, wasu mahukunta ne a kotunan ko kuma a ma’aikatun gwamnatin jihar, suka bayar da umarnin a cire na’urorin domin a yi masu gyara.

A cewarsa, shi ne ya sace na’urar sanyaya kotun Majistari da ke a Unguwar Barnawa, inda ya kara da cewa, shi ne, ya sace wata na’urar sanyaya kotun da ke kan titin Ibrahin Taiwo, ya kuma je wata kotu ta shida da nufin sace wata na’urar kotun, amma ba a bashi damar dauka ba

Sannan ya je majalisar dokokin jihar, inda a nan ma, ya saci wata na’urar.

Labarai Masu Nasaba

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

Bugu da kari, ya kuma shiga kotu ta shida da nufin sace wata, amma wasu masu aiki a kotun, suka ce sai na kawo musu takardar izninin kwacewa da dauka.

Ya ce, bayan da na nuna masu masu takardar sai ma’aikatan suka duba takardar, suka ce min ta bogi ce, wanda hakan ya sanya ba su bani damar kwance na’urar ba, ni kuma ban da wata masaniyar cewar ta bogi ce.

“Ban samu nasarar dauka a nan ba, na kira Ismai’ila a waya na shaida masa, sai ya umarce ni cewa, in wuce zuwa kotun Ibrahim Taiwao in kwanto wasu na’urorin, in ji shi.

A cewarsa, asiransa ya tuno ne, bayan da ya samu nasarar kwance na’urorin ya loda su a cikin wani Keke Napape da ya dauko haya, inda wasu ‘yan sanda a kan hanya suka tare Keken, suka kama kayan suka ce sai na kira wanda ya turo ni in dauki kayan.

Ya ce, “ ‘Yan sandan sun tafi da ni, suka rufe ni a caji ofis, suka ce, in kira wanda ya turo ni, na kira wayarsa na sheda masu cewa, an kama ni, sai ya kashe wayarsa, ni kuma ban san inda zan gan shi ba, laifi dai, na aikata, ina neman a yi min afuwa.

Da yake yi wa manema labarai bayani kan batun, ASP Mansur ya ce, matashin yana zuwa yin satar ce da yaudara, inda ya kara da cewa, kafin ya je yin satar, sai bayan ya gama samun sirrin yadda wajen yake.

Ya ce, jami’an ‘yan sandan rundunar sun kuma kwato kayan da yaron ya sace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ACKotuMatashiSata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rungumar Harkar Noma Mafita Ce Ga Ma’aikata Masu Ritaya

Next Post

‘Dalilin Da Ya Sa ‘Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

Related

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

5 days ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

5 days ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

5 days ago
An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

1 month ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

1 month ago
Next Post
‘Dalilin Da Ya Sa ‘Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

‘Dalilin Da Ya Sa 'Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

August 21, 2025
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

August 21, 2025
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.