• English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matashin Da Ya Kware Wajen Satar Na’urorin AC A Kotu, Ya Fada Komar ‘Yansanda

by Abubakar Abba
1 year ago
Matashin

Wani matashi dan shekara 20, mai suna Mohammed Sani da ake zargin ya kware wajen sace-sacen na’urorin sanyaya dakuna wato AC a kotuna jihar, ya fada a komar rundunar ‘yansandan Jihar Kaduna.

A yayin da kakakin rundunar ‘yansandan jihar ASP Mansur Hassan ya bajen kolin Sani a gaban ‘yan jairida, Sani ya shedawa ‘yan jaridar cewa, ya kware wajen satar na’urorin a kutuna da kuma na wasu ofis-ofis na gwamnatin jihar.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • Sin Ta Shirya Daukar Baje Kolin CIIE A Matsayin Wata Dama Ta Gabatar Da Damarmakin Babbar Kasuwarta Ga Duniya

Yaron ya yi ikirarin cewa, wani uban gidansa ne mai suna Isma’il, ke tura shi yin satar ta hanyar bashi wata takarda da ke nuna cewa, wasu mahukunta ne a kotunan ko kuma a ma’aikatun gwamnatin jihar, suka bayar da umarnin a cire na’urorin domin a yi masu gyara.

A cewarsa, shi ne ya sace na’urar sanyaya kotun Majistari da ke a Unguwar Barnawa, inda ya kara da cewa, shi ne, ya sace wata na’urar sanyaya kotun da ke kan titin Ibrahin Taiwo, ya kuma je wata kotu ta shida da nufin sace wata na’urar kotun, amma ba a bashi damar dauka ba

Sannan ya je majalisar dokokin jihar, inda a nan ma, ya saci wata na’urar.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

Bugu da kari, ya kuma shiga kotu ta shida da nufin sace wata, amma wasu masu aiki a kotun, suka ce sai na kawo musu takardar izninin kwacewa da dauka.

Ya ce, bayan da na nuna masu masu takardar sai ma’aikatan suka duba takardar, suka ce min ta bogi ce, wanda hakan ya sanya ba su bani damar kwance na’urar ba, ni kuma ban da wata masaniyar cewar ta bogi ce.

“Ban samu nasarar dauka a nan ba, na kira Ismai’ila a waya na shaida masa, sai ya umarce ni cewa, in wuce zuwa kotun Ibrahim Taiwao in kwanto wasu na’urorin, in ji shi.

A cewarsa, asiransa ya tuno ne, bayan da ya samu nasarar kwance na’urorin ya loda su a cikin wani Keke Napape da ya dauko haya, inda wasu ‘yan sanda a kan hanya suka tare Keken, suka kama kayan suka ce sai na kira wanda ya turo ni in dauki kayan.

Ya ce, “ ‘Yan sandan sun tafi da ni, suka rufe ni a caji ofis, suka ce, in kira wanda ya turo ni, na kira wayarsa na sheda masu cewa, an kama ni, sai ya kashe wayarsa, ni kuma ban san inda zan gan shi ba, laifi dai, na aikata, ina neman a yi min afuwa.

Da yake yi wa manema labarai bayani kan batun, ASP Mansur ya ce, matashin yana zuwa yin satar ce da yaudara, inda ya kara da cewa, kafin ya je yin satar, sai bayan ya gama samun sirrin yadda wajen yake.

Ya ce, jami’an ‘yan sandan rundunar sun kuma kwato kayan da yaron ya sace.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
Next Post
‘Dalilin Da Ya Sa ‘Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

‘Dalilin Da Ya Sa 'Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

LABARAI MASU NASABA

Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.