ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matashin Da Ya Kware Wajen Satar Na’urorin AC A Kotu, Ya Fada Komar ‘Yansanda

by Abubakar Abba
2 years ago
Matashin

Wani matashi dan shekara 20, mai suna Mohammed Sani da ake zargin ya kware wajen sace-sacen na’urorin sanyaya dakuna wato AC a kotuna jihar, ya fada a komar rundunar ‘yansandan Jihar Kaduna.

A yayin da kakakin rundunar ‘yansandan jihar ASP Mansur Hassan ya bajen kolin Sani a gaban ‘yan jairida, Sani ya shedawa ‘yan jaridar cewa, ya kware wajen satar na’urorin a kutuna da kuma na wasu ofis-ofis na gwamnatin jihar.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • Sin Ta Shirya Daukar Baje Kolin CIIE A Matsayin Wata Dama Ta Gabatar Da Damarmakin Babbar Kasuwarta Ga Duniya

Yaron ya yi ikirarin cewa, wani uban gidansa ne mai suna Isma’il, ke tura shi yin satar ta hanyar bashi wata takarda da ke nuna cewa, wasu mahukunta ne a kotunan ko kuma a ma’aikatun gwamnatin jihar, suka bayar da umarnin a cire na’urorin domin a yi masu gyara.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, shi ne ya sace na’urar sanyaya kotun Majistari da ke a Unguwar Barnawa, inda ya kara da cewa, shi ne, ya sace wata na’urar sanyaya kotun da ke kan titin Ibrahin Taiwo, ya kuma je wata kotu ta shida da nufin sace wata na’urar kotun, amma ba a bashi damar dauka ba

Sannan ya je majalisar dokokin jihar, inda a nan ma, ya saci wata na’urar.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Bugu da kari, ya kuma shiga kotu ta shida da nufin sace wata, amma wasu masu aiki a kotun, suka ce sai na kawo musu takardar izninin kwacewa da dauka.

Ya ce, bayan da na nuna masu masu takardar sai ma’aikatan suka duba takardar, suka ce min ta bogi ce, wanda hakan ya sanya ba su bani damar kwance na’urar ba, ni kuma ban da wata masaniyar cewar ta bogi ce.

“Ban samu nasarar dauka a nan ba, na kira Ismai’ila a waya na shaida masa, sai ya umarce ni cewa, in wuce zuwa kotun Ibrahim Taiwao in kwanto wasu na’urorin, in ji shi.

A cewarsa, asiransa ya tuno ne, bayan da ya samu nasarar kwance na’urorin ya loda su a cikin wani Keke Napape da ya dauko haya, inda wasu ‘yan sanda a kan hanya suka tare Keken, suka kama kayan suka ce sai na kira wanda ya turo ni in dauki kayan.

Ya ce, “ ‘Yan sandan sun tafi da ni, suka rufe ni a caji ofis, suka ce, in kira wanda ya turo ni, na kira wayarsa na sheda masu cewa, an kama ni, sai ya kashe wayarsa, ni kuma ban san inda zan gan shi ba, laifi dai, na aikata, ina neman a yi min afuwa.

Da yake yi wa manema labarai bayani kan batun, ASP Mansur ya ce, matashin yana zuwa yin satar ce da yaudara, inda ya kara da cewa, kafin ya je yin satar, sai bayan ya gama samun sirrin yadda wajen yake.

Ya ce, jami’an ‘yan sandan rundunar sun kuma kwato kayan da yaron ya sace.

Matashin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
‘Dalilin Da Ya Sa ‘Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

‘Dalilin Da Ya Sa 'Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.