ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matashin Da Ya Kware Wajen Satar Na’urorin AC A Kotu, Ya Fada Komar ‘Yansanda

by Abubakar Abba
2 years ago
Matashin

Wani matashi dan shekara 20, mai suna Mohammed Sani da ake zargin ya kware wajen sace-sacen na’urorin sanyaya dakuna wato AC a kotuna jihar, ya fada a komar rundunar ‘yansandan Jihar Kaduna.

A yayin da kakakin rundunar ‘yansandan jihar ASP Mansur Hassan ya bajen kolin Sani a gaban ‘yan jairida, Sani ya shedawa ‘yan jaridar cewa, ya kware wajen satar na’urorin a kutuna da kuma na wasu ofis-ofis na gwamnatin jihar.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • Sin Ta Shirya Daukar Baje Kolin CIIE A Matsayin Wata Dama Ta Gabatar Da Damarmakin Babbar Kasuwarta Ga Duniya

Yaron ya yi ikirarin cewa, wani uban gidansa ne mai suna Isma’il, ke tura shi yin satar ta hanyar bashi wata takarda da ke nuna cewa, wasu mahukunta ne a kotunan ko kuma a ma’aikatun gwamnatin jihar, suka bayar da umarnin a cire na’urorin domin a yi masu gyara.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, shi ne ya sace na’urar sanyaya kotun Majistari da ke a Unguwar Barnawa, inda ya kara da cewa, shi ne, ya sace wata na’urar sanyaya kotun da ke kan titin Ibrahin Taiwo, ya kuma je wata kotu ta shida da nufin sace wata na’urar kotun, amma ba a bashi damar dauka ba

Sannan ya je majalisar dokokin jihar, inda a nan ma, ya saci wata na’urar.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

Bugu da kari, ya kuma shiga kotu ta shida da nufin sace wata, amma wasu masu aiki a kotun, suka ce sai na kawo musu takardar izninin kwacewa da dauka.

Ya ce, bayan da na nuna masu masu takardar sai ma’aikatan suka duba takardar, suka ce min ta bogi ce, wanda hakan ya sanya ba su bani damar kwance na’urar ba, ni kuma ban da wata masaniyar cewar ta bogi ce.

“Ban samu nasarar dauka a nan ba, na kira Ismai’ila a waya na shaida masa, sai ya umarce ni cewa, in wuce zuwa kotun Ibrahim Taiwao in kwanto wasu na’urorin, in ji shi.

A cewarsa, asiransa ya tuno ne, bayan da ya samu nasarar kwance na’urorin ya loda su a cikin wani Keke Napape da ya dauko haya, inda wasu ‘yan sanda a kan hanya suka tare Keken, suka kama kayan suka ce sai na kira wanda ya turo ni in dauki kayan.

Ya ce, “ ‘Yan sandan sun tafi da ni, suka rufe ni a caji ofis, suka ce, in kira wanda ya turo ni, na kira wayarsa na sheda masu cewa, an kama ni, sai ya kashe wayarsa, ni kuma ban san inda zan gan shi ba, laifi dai, na aikata, ina neman a yi min afuwa.

Da yake yi wa manema labarai bayani kan batun, ASP Mansur ya ce, matashin yana zuwa yin satar ce da yaudara, inda ya kara da cewa, kafin ya je yin satar, sai bayan ya gama samun sirrin yadda wajen yake.

Ya ce, jami’an ‘yan sandan rundunar sun kuma kwato kayan da yaron ya sace.

Matashin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna

June 6, 2026
Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID
Kotu Da Ɗansanda

An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

June 6, 2026
NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Sallami Ma’aikatan Sa-kai Biyar A Kano Saboda Rashin Da’a

June 6, 2026
Next Post
‘Dalilin Da Ya Sa ‘Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

‘Dalilin Da Ya Sa 'Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026
Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

June 8, 2026
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

June 8, 2026
Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

June 8, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.