• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Masu Noman Albasa Ke Samun Karamar Riba A Nijeriya?

by Abubakar Abba
1 year ago
Albasa

Hukumar kula da fitar kaya ta kasa (NEPC), ta nuna damuwarta kan rashin samun riba mai yawa daga hada-hadar kasuwancin Alabsar, duk kuwa da cewa; Nijeriya na daya daga cikin kasashen da ke gaba a fadin Afirka wajen nomanta.    

Duk da cewa, a duk shekara ana noman Albasa kimanin tan miliyan biyu, amma adadin Albasar da ake nomawa a kasar ya yi matukar yin kasa, wanda hakan na faruwa ne sakamakon amfani da gundarin Albasar wajen yin wasu nau’ikan abubuwa daban-daban a wannan kasa.

  • Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya
  • Zaben Gwamna: Kallo Ya Koma Jihar Edo

Hai ila yau, masu ruwa da tsaki ne suka bayyana haka; a wani taron tattauwa a kan dabarun bunkasa nomanta da aka gudanar a Jihar Gombe.

Babbar Darakta ta hukumar NEPC, Nonye Ayeni a jawabinta a wajen taron, ta bayyana kalubalen da ake fuskanta a bangaren hada-hadar kasuwancin Albasar a Nijeriya.

Kazalika, ta sanar da haka ne; ta hanyar wakilinta a wajen taron Mustapha Umar Faruk, inda ya bayyana cewa; an jawo jihohi kamar su Gombe, Sakkwato, Kebbi, Zamfara, Katsina, Kano, Kaduna, Jigawa, Yobe, Borno, Bauchi, Taraba, Filato da kuma Abuja, a wannan fanni na noman Albasar.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Ta ci gaba da cewa, sai dai har yanzu Nijeriya ta gaza ci gaba da rike matsayinta a faninn hada-hadar kasuwancin na Albasa, musamman sakamakon rashin iya sarrafa ta da kuma yin amfani da dabarun fitar da ita zuwa kasashen ketare.

Nonye ta kara da cewa, saboda rashin kimanta Albsar a kasar nan ne, yasa ake samun raguwar samun ribarta da kuma raguwar saumun kudaden shiga daga fitar da ita da ake yi zuwa kasashen ketare.

A cewarta, wannan dalili ne yasa hukumar ta hanyar wannan shiri ta samu nasarar tattaunawa da masu ruwa da tsaki, domin bunkasa dabarun fitar da ita zuwa kasashen ketare.

A cewar tata, hakan zai bai wa Nijeriya damar aiwatar da gasa a kasuwannin duniya, musamman a wannan bangare na hada-hadar kasuwancin Albasa, a tsakaninta da sauran kasashen duniya.

Nasiru Aliyu, Kwamishina Ma’aikatar Kasuwanci da Zuba Jari; yaba wa hukumar ya yi a kan shirya taron. Inda ya sanar da cewa, taron ya zo a kan gaba duba da karuwar wayar da kan manoman Albasar.

Kwamishinan, wanda Babban Sakatare a Ma’aikatar; Babayo Hassan Abubakar ya wakilta a wajen taron, ya bukaci manomanta su kara yin kokari wajen noma ta; ba tare da dogaro ga gwamnati ba.

Shi kuwa, Shugaban Kungiyar Manoman Albasa na Shiyyar Arewa Maso Gabas; Alhaji Sani Pantami; yaba wa hukumar ya yi a kan ilimantar da manoman da sauran masu ruwa da tsaki da ta yi, musamman a kan muhimmancin kasuwancin Albasa na kasa da kasa.

Ya kuma yi waiwaye a kan kalubalen da manoman suke fuskanta a baya, da suka hada da yin asara sakamakon rashin kwarewar da suke da ita na fitar da Albasar zuwa kasashen na ketare, domin sayar da ita.

Sai dai, ya yi nuni da cewa; bisa ilimin da suka samu ta hanyar shirin ya ce, yana da yakinin cewa; akasarin manoman a halin yanzu zai ba su kwarin gwiwar sanin dabarun noman Albasar, musamman ta hanyar samun ingantaccen Irin nomanta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Next Post
Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (6)

Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu (6)

LABARAI MASU NASABA

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.