ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ya Kamata Kasashen Afirka Su Bunkasa Tattalin Arziki Tare Da Kare Muhalli?

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 week ago
Muhalli

Cikin manufofin raya kasa na Najeriya da na sauran kasashen dake nahiyar Afirka, duk an ambato cewa za a yi kokarin raya tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba. Sai dai, a wani lokaci a kan ga yadda mutane suke shakku game da batun, suna tambaya cewa: Me ya sa muke ware kudi ga bangaren kare muhalli, duk da cewa ana matukar bukatar raya tattalin arziki cikin gaggawa a Afirka?

Tun da akwai tambaya, to, ya kamata mu nemi amsa, da cimma matsaya, maimakon kai-komo tsakanin mabambantan manufofi. A wannan wata da muke ciki, aka cika shekaru 10 da kasashen duniya suka sa hannu kan yarjejeniyar Paris ta tinkarar sauyawar yanayin duniya. A cikin shekarun 10 da suka wuce, matakan da mutanen duniya suka dauka a hadin gwiwarsu sun rage adadin hauhawar zafin yanayin da ake sa ran samu daga digiri 4 zuwa digiri 2.8, bisa ma’aunin Celcius, duk da cewa bai kai digiri 1.5 da ake son samu ba. Kana wani babban dalilin da ya hana dan Adam samun biyan bukata a wannan karo, shi ne wasu kasashe suna amai suna lashewa a fannin aiwatar da matakan kare muhalli. Misali, kasar Amurka ta taba janye jikinta daga yarjejeniyar Paris har sau biyu, kuma har yanzu ba ta amince da yarjejeniyar ba, ko da yake kasar ce ke fitar da mafi yawan iska mai dumama yanayi a tarihin dan Adam.

Sai dai me ya sa ake bukatar raya tattalin arziki tare da kare muhalli?

ADVERTISEMENT

Dalili na farko shi ne, babu sabani a tsakanin batutuwan 2, wato kare muhalli da bunkasa tattalin arziki.

Wani rahoton da dandalin tattaunawa kan tattalin arzikin duniya ya fitar a kwanan baya, ya ce darajar tattalin arziki mai alaka da batun kare muhalli a duk duniya ta riga ta zarce dalar Amurka triliyan 5 a shekarar 2024, adadin da zai haura triliyan 7 a shekarar 2030. Wato wannan bangare yana cikin fannoni mafi samun karuwar daraja a duk duniya.

LABARAI MASU NASABA

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?

Me Ya Sa Aka Kayyade Yin Amfani Da Sinadaran Narkar Da Kankara A Beijing

Sa’an nan idan mun dauki kasar Sin a matsayin misali, to, za mu ga kasar tana tsayawa kan manufarta ta “Daukar muhalli mai inganci a matsayin damar samun ci gaban tattalin arziki”, inda sana’o’i masu alaka da kare muhalli suka zama muhimmin karfin da ke sa kaimin tattalin arzikin kasar. Kana ana hasashen cewa, darajar bangaren sana’o’in kare muhalli na kasar Sin za ta kai dalar Amurka triliyan 2.12, nan da shekarar 2030.

Kana dalili na biyu da ya sa ake kokarin kare muhalli a kasashen Afirka, shi ne, akwai dimbin albarkatu a yankunansu, wadanda za a iya amfani da su wajen raya tattalin arziki tare da kare muhalli.

Idan mun dauki bangaren makamashi a matsayin misali: Daukacin karfin ruwa a nahiyar Afirka ya kai Megawatts miliyan 115.5, wanda ya ninka karfin tashoshin samar da wutar lantarki ta karfin ruwa da aka gina a Afirka har sau 34. An ce idan an samu damar amfani da karfin ruwa sosai, to, ko kogin Congo shi kadai ma zai iya biyan bukatar daukacin nahiyar Afirka a fannin wutar lantarki a yanzu. Ban da haka, kasashen Afirka suna da cikakken boyayyen karfi a fannin samar da wutar lantarki ta zafin rana, da karfin iska, da sauran makamashi masu tsabta. Bisa hasashen da hukumomin kasa da kasa masu kula da makamashin da ake iya sabuntawa suka yi, ya zuwa shekarar 2030, karfin samar da wutar lantarki ta wannan nau’in makamashi a nahiyar Afirka zai kai Gigawatts 310, adadin da zai kasance kan gaba a duniya.

Sa’an nan, dalili na uku na dacewar manufar kare muhalli ta kasashen Afirka, shi ne, kasashen suna samun cikakken goyon baya daga kasar Sin a wannan fanni.

Dimbin misalai sun shaida cewa, kamfanonin kasar Sin suna taka rawar gani wajen taimakon kasashen Afirka raya tattalin arzikinsu ta wasu dabaru masu kare muhalli. Haka zalika, kasar Sin tana kokarin gabatar da fasahohin zamani na kare muhalli ga kasashen Afirka, karkashin tsarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa a duniya.

Duk wadannan dalilan da muka ambata sun nuna cewa, aikin raya tattalin arziki tare da kare muhalli a nahiyar Afirka na da makoma mai haske. Don haka, kamata ya yi, a tsaya kan hadin gwiwa tare da abokan hulda don raya tattalin arzikin kasashen Afirka ta wasu dabaru masu kare muhalli, ta yadda za a iya tabbatar da ci gaban tattalin arzikin kasashen, gami da samar da gudunmowa ga yunkurin tinkarar sauyawar yanayi a duniya. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za A Iya Tabbatar Da Tsaro A Yammacin Afirka?

December 17, 2025
Me Ya Sa Aka Kayyade Yin Amfani Da Sinadaran Narkar Da Kankara A Beijing
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Kayyade Yin Amfani Da Sinadaran Narkar Da Kankara A Beijing

December 16, 2025
Waiwaye Adon Tafiya : Tasirin Sin A Kan Afirka Ta Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Waiwaye Adon Tafiya : Tasirin Sin A Kan Afirka Ta Fannin Fasahar AI

December 15, 2025
Next Post
An Yi Barazanar Kashe Ni Bayan Komawa Manchester United – Rooney

An Yi Barazanar Kashe Ni Bayan Komawa Manchester United - Rooney

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.