ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ya Kamata Kasashen Afirka Su Bunkasa Tattalin Arziki Tare Da Kare Muhalli?

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Muhalli

Cikin manufofin raya kasa na Najeriya da na sauran kasashen dake nahiyar Afirka, duk an ambato cewa za a yi kokarin raya tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba. Sai dai, a wani lokaci a kan ga yadda mutane suke shakku game da batun, suna tambaya cewa: Me ya sa muke ware kudi ga bangaren kare muhalli, duk da cewa ana matukar bukatar raya tattalin arziki cikin gaggawa a Afirka?

Tun da akwai tambaya, to, ya kamata mu nemi amsa, da cimma matsaya, maimakon kai-komo tsakanin mabambantan manufofi. A wannan wata da muke ciki, aka cika shekaru 10 da kasashen duniya suka sa hannu kan yarjejeniyar Paris ta tinkarar sauyawar yanayin duniya. A cikin shekarun 10 da suka wuce, matakan da mutanen duniya suka dauka a hadin gwiwarsu sun rage adadin hauhawar zafin yanayin da ake sa ran samu daga digiri 4 zuwa digiri 2.8, bisa ma’aunin Celcius, duk da cewa bai kai digiri 1.5 da ake son samu ba. Kana wani babban dalilin da ya hana dan Adam samun biyan bukata a wannan karo, shi ne wasu kasashe suna amai suna lashewa a fannin aiwatar da matakan kare muhalli. Misali, kasar Amurka ta taba janye jikinta daga yarjejeniyar Paris har sau biyu, kuma har yanzu ba ta amince da yarjejeniyar ba, ko da yake kasar ce ke fitar da mafi yawan iska mai dumama yanayi a tarihin dan Adam.

Sai dai me ya sa ake bukatar raya tattalin arziki tare da kare muhalli?

ADVERTISEMENT

Dalili na farko shi ne, babu sabani a tsakanin batutuwan 2, wato kare muhalli da bunkasa tattalin arziki.

Wani rahoton da dandalin tattaunawa kan tattalin arzikin duniya ya fitar a kwanan baya, ya ce darajar tattalin arziki mai alaka da batun kare muhalli a duk duniya ta riga ta zarce dalar Amurka triliyan 5 a shekarar 2024, adadin da zai haura triliyan 7 a shekarar 2030. Wato wannan bangare yana cikin fannoni mafi samun karuwar daraja a duk duniya.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Sa’an nan idan mun dauki kasar Sin a matsayin misali, to, za mu ga kasar tana tsayawa kan manufarta ta “Daukar muhalli mai inganci a matsayin damar samun ci gaban tattalin arziki”, inda sana’o’i masu alaka da kare muhalli suka zama muhimmin karfin da ke sa kaimin tattalin arzikin kasar. Kana ana hasashen cewa, darajar bangaren sana’o’in kare muhalli na kasar Sin za ta kai dalar Amurka triliyan 2.12, nan da shekarar 2030.

Kana dalili na biyu da ya sa ake kokarin kare muhalli a kasashen Afirka, shi ne, akwai dimbin albarkatu a yankunansu, wadanda za a iya amfani da su wajen raya tattalin arziki tare da kare muhalli.

Idan mun dauki bangaren makamashi a matsayin misali: Daukacin karfin ruwa a nahiyar Afirka ya kai Megawatts miliyan 115.5, wanda ya ninka karfin tashoshin samar da wutar lantarki ta karfin ruwa da aka gina a Afirka har sau 34. An ce idan an samu damar amfani da karfin ruwa sosai, to, ko kogin Congo shi kadai ma zai iya biyan bukatar daukacin nahiyar Afirka a fannin wutar lantarki a yanzu. Ban da haka, kasashen Afirka suna da cikakken boyayyen karfi a fannin samar da wutar lantarki ta zafin rana, da karfin iska, da sauran makamashi masu tsabta. Bisa hasashen da hukumomin kasa da kasa masu kula da makamashin da ake iya sabuntawa suka yi, ya zuwa shekarar 2030, karfin samar da wutar lantarki ta wannan nau’in makamashi a nahiyar Afirka zai kai Gigawatts 310, adadin da zai kasance kan gaba a duniya.

Sa’an nan, dalili na uku na dacewar manufar kare muhalli ta kasashen Afirka, shi ne, kasashen suna samun cikakken goyon baya daga kasar Sin a wannan fanni.

Dimbin misalai sun shaida cewa, kamfanonin kasar Sin suna taka rawar gani wajen taimakon kasashen Afirka raya tattalin arzikinsu ta wasu dabaru masu kare muhalli. Haka zalika, kasar Sin tana kokarin gabatar da fasahohin zamani na kare muhalli ga kasashen Afirka, karkashin tsarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa a duniya.

Duk wadannan dalilan da muka ambata sun nuna cewa, aikin raya tattalin arziki tare da kare muhalli a nahiyar Afirka na da makoma mai haske. Don haka, kamata ya yi, a tsaya kan hadin gwiwa tare da abokan hulda don raya tattalin arzikin kasashen Afirka ta wasu dabaru masu kare muhalli, ta yadda za a iya tabbatar da ci gaban tattalin arzikin kasashen, gami da samar da gudunmowa ga yunkurin tinkarar sauyawar yanayi a duniya. (Bello Wang)

Muhalli
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Muhalli
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
An Yi Barazanar Kashe Ni Bayan Komawa Manchester United – Rooney

An Yi Barazanar Kashe Ni Bayan Komawa Manchester United - Rooney

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.