• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Tara Wa Dan Takarar Gwamnanmu Miliyan 511 A Kano – NNPP

by Sadiq
3 years ago
NNPP

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta kaddamar da shirin tara kudade ga jama’a domin yakin neman zaben dan takarar gwamnanta na jihar, Abba Kabiru Yusuf wanda aka fi sani da “Abba Gida”.

A wajen taron liyafar cin abinci na musamman da jam’iyyar ta shirya domin samun tallafin kudi daga ‘ya’yan jam’iyyar, NNPP ta ce an samu sama da Naira miliyan 511, wanda kaso mafi tsoka ya fito ne daga dan majalisa mai wakiltar Tofa/Dawakin-Tofa/Rimin-Gado a zauren majalisar wakilai Tijjani Abdulkadir Jobe wanda ya bada gudunmawar Naira miliyan 50.

  • Duniya Ta Shiga Alhinin Mutuwar Sama Da Mutum 3,000 A Turkiyya Da Siriya
  • An Gurfanar Da ‘Yan Bangar Siyasa 10 A Gaban Kotu A Sakkwato 

Da yake jawabi a wajen liyafar, shugaban masu bayar da tallafi kuma tsohon mai taimaka wa shugaban kasa, Abdulrahman Kawu Sumaila ya bayyana cewa NNPP ta himmatu wajen fara yakin neman zabe da goyon bayan mambobin jam’iyyar.

Tsohon dan majalisar wakilan, ya karyata zargin sayen kuri’u da magudin zabe sannan ya kara da cewa jama’a sun taru ne domin su bayar da nasu tallafin.

Sumaila ya kara da cewa ’yan jam’iyyar NNPP masu sadaukarwa ne saboda suna da akidar Kwankwasiyya da ba ta da kudi.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ya kara da cewa NNPP ta shirya tsaf domin kwato Kano daga jam’iyyar APC mai mulki a zaben gwamna da za a yi a wata mai zuwa.

“Zabe na karatowa kuma NNPP ba ta buri face kwato Kano. Mun taru a matsayinmu na NNPP da iyalan Kwankwasiyya don tattara kayan aiki don yakin neman zaben gwamna,” in ji Sumaila.

“Yanzu, cikin kasa da sa’o’i uku, mun samu tallafin jama’a sama da Naira miliyan 500 kuma har yanzu muna ci gaba da karbar tallafin. Kamar yadda kuka sani ba ma cikin gwamnati don haka ba mu da wani gata da asusun gwamnati don haka ne muke bude wannan taron jama’a inda muka nemi tallafi.

Dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf, ya yaba da goyon bayan mambobin da suka bayar da gudunmawarsu, inda ya ce NNPP ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen gudanar da ayyukan al’umma idan har aka zabe su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta
Siyasa

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Siyasa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
Siyasa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum Daya, Sun Sace 10 A Jihar Neja

'Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum Daya, Sun Sace 10 A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.