• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Tara Wa Dan Takarar Gwamnanmu Miliyan 511 A Kano – NNPP

by Sadiq
2 years ago
in Siyasa
0
Mun Tara Wa Dan Takarar Gwamnanmu Miliyan 511 A Kano – NNPP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta kaddamar da shirin tara kudade ga jama’a domin yakin neman zaben dan takarar gwamnanta na jihar, Abba Kabiru Yusuf wanda aka fi sani da “Abba Gida”.

A wajen taron liyafar cin abinci na musamman da jam’iyyar ta shirya domin samun tallafin kudi daga ‘ya’yan jam’iyyar, NNPP ta ce an samu sama da Naira miliyan 511, wanda kaso mafi tsoka ya fito ne daga dan majalisa mai wakiltar Tofa/Dawakin-Tofa/Rimin-Gado a zauren majalisar wakilai Tijjani Abdulkadir Jobe wanda ya bada gudunmawar Naira miliyan 50.

  • Duniya Ta Shiga Alhinin Mutuwar Sama Da Mutum 3,000 A Turkiyya Da Siriya
  • An Gurfanar Da ‘Yan Bangar Siyasa 10 A Gaban Kotu A Sakkwato 

Da yake jawabi a wajen liyafar, shugaban masu bayar da tallafi kuma tsohon mai taimaka wa shugaban kasa, Abdulrahman Kawu Sumaila ya bayyana cewa NNPP ta himmatu wajen fara yakin neman zabe da goyon bayan mambobin jam’iyyar.

Tsohon dan majalisar wakilan, ya karyata zargin sayen kuri’u da magudin zabe sannan ya kara da cewa jama’a sun taru ne domin su bayar da nasu tallafin.

Sumaila ya kara da cewa ’yan jam’iyyar NNPP masu sadaukarwa ne saboda suna da akidar Kwankwasiyya da ba ta da kudi.

Labarai Masu Nasaba

2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Ya kara da cewa NNPP ta shirya tsaf domin kwato Kano daga jam’iyyar APC mai mulki a zaben gwamna da za a yi a wata mai zuwa.

“Zabe na karatowa kuma NNPP ba ta buri face kwato Kano. Mun taru a matsayinmu na NNPP da iyalan Kwankwasiyya don tattara kayan aiki don yakin neman zaben gwamna,” in ji Sumaila.

“Yanzu, cikin kasa da sa’o’i uku, mun samu tallafin jama’a sama da Naira miliyan 500 kuma har yanzu muna ci gaba da karbar tallafin. Kamar yadda kuka sani ba ma cikin gwamnati don haka ba mu da wani gata da asusun gwamnati don haka ne muke bude wannan taron jama’a inda muka nemi tallafi.

Dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf, ya yaba da goyon bayan mambobin da suka bayar da gudunmawarsu, inda ya ce NNPP ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen gudanar da ayyukan al’umma idan har aka zabe su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Gida-gidakanoMiliyan 511NNPPTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kisan Katsina: Mun Rasa Rayuka 102 -Shugaban Al’umma 

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum Daya, Sun Sace 10 A Jihar Neja

Related

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Labarai

2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC

15 hours ago
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
Siyasa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

2 days ago
Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC
Siyasa

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

3 days ago
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

3 days ago
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai
Labarai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

4 days ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

5 days ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum Daya, Sun Sace 10 A Jihar Neja

'Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum Daya, Sun Sace 10 A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

July 31, 2025
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

July 31, 2025
NIN-SIM: Masu Hulda Da Kamfanonin Sadarwa Sun Koka Kan Katse Layinsu Daga Tsarin Kira

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

July 31, 2025
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

July 31, 2025
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

July 31, 2025
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

July 31, 2025
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

July 31, 2025
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

July 31, 2025
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

July 31, 2025
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.