• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk

by Aisha Idris Abdullahi (ALEESHAT) and Sulaiman
7 months ago
in Adabi
0
Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shafin ADABI shafi ne daya saba zakulo muku fitattun marubuta littattafan hausa har ma da masu tasowa domin jin ta bakinsu game da abin da ya shafi rubutunsu.

A yau ma shafi na tafe da wata bakuwar marubuciyar wato; MARYAM FARUK wacce aka fi sani da UMMU MAHEER inda ta bayyanawa masu karatu batutuwa masu yawan gaske da suka shafi rayuwarta da kuma rubutunta. Ga dai tattaunawar tare da wakiliyarmu AISHA IDRIS ABDULLAHI (ALEESHAT) Kamar haka;

Wane labari ne ya zamo bakandamiyarki?

Wata Kishiyar.

 

Labarai Masu Nasaba

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

Wane labari ne ya fi baki wahala wajen rubutawa?

A cikin rubutuna wanda ya fi ba ni wahala shi ne; MATAR MUTUM. Dalili; labarin ya kunshi ‘characters’ da yawa masu mabanbantan halaye. da yawan marubuta sukan rude a rubutu har ta kai sukan canza dabi’un jarumai idan tafiya tayi nisa ba tare da saninsu ba. Akwai bukatar nutsuwa sosai. A sanda nake rubutun wani sa’in sai na koma nayo karatun baya a kokarin ganin komai ya tafi mun daidai ba tare da na canza akala ko na shigar da abun da babu shi a halayyar wani ba hakan ya sa rubutun bai yi mun sauri ba ga kuma tarin makaranta dake dakon jiransa a kullum.

 

Wane irin nasarori ki ka samu game da rubutu?

Alhamdulillah. Ta dalilin rubutu na hadu da mutanen kirki wanda ba dan rubutu ba babu lallai in sansu a rayuwata. Rubutu ya ba ni sababbin iyaye, yayye, kanne, kawaye har da aminai. Rubutu ya kai sunana inda ni ban je ba ciki da wajen kasar nan Alhamdulillah.

 

Wane abu ne ya taba faruwa da ke na farin ciki ko akasin haka wanda ba za ki taba mantawa da shi ba game da rubutu?

Abin farin ciki yanda mutane suke kirana a waya su yi mun addu’a da fatan alkhairi akan yadda rubutu na ya shafi rayuwarsu ya kuma haska musu mafita cikin wani abu daya damesu yana matukar saka ni farin ciki.

 

Kin taba kuka sanadiyyar rubutu ko karatu?

A dabi’ance dama ni mutum ce me saurin kuka, sannan salon rubutuna ina yinsa yanda makaranci zai ji tamkar a gabansa koma a karankansa abun da yake karantawa yake faruwa. A sanda nake rubuta littafin MATAR MUTUM episode din rasuwar AHMAD BECHI sai da nayi sati a kullum na dauki abin rubutu zan fara sai in kasa kukan tausayin al’amarin ya hanani haka bayan da nayi ‘publishing episode’ din har sai da na ji kamar in gogeta daga cikin littafin saboda yadda ta famawa mutane da yawa mikin rashin makusantansu. Tamkar gaske haka muka yi kukan rashin Ahmad sai da muka shafe kwanaki muna zaman makoki kafin muka ci gaba.

 

Kamar wane lokaci ki ka fi jin dadin yin rubutu?

Na fi jin dadin rubutu da rana bayan na gama ayyukan gida na gaji saboda ban iya baccin rana ba dan haka sai in yi amfani da wannan lokacin nayi rubutu, wani lokacin na kan yi da daddare sai dai nafi jin dadi da rana gaskiya.

 

Bayan rubutu kina yin wata sana’ar?

Ina kasuwanci sannan ina koyarwa, karfe sha daya nake shiga makaranta na tashi karfe biyu, dan haka a ranakun makaranta kafin na fita nake yin duk wani aikin gida kasuwnaci kuma a cikin gida ne ina siyar da kayayyakin sakawa dana amfani kusan duk abin da nake bukatar siya ta waya ne zan zaba a kawo mun duk da akwai abubuwan da suke bukatar dole sai naje kasuwa da kaina kamar idan zan yi hijabai nafi so in je in zabo yadi da kaina.

 

Wacce marubuciya ce take burge ki tun kafin ki fara rubutu?

Anti Fauziyya D. Sulaiman ita ce ‘role model’ dina a rubutu, kuma har yau Allah bai saka na taba magana da ita ko na ganta a zahiri ba.

 

Wace ce babbar kawarki a marubuta?

Suna da yawa.

 

Wacce shawara za ki bawa masu karatu har ma da sauran ‘yan’uwanki marubuta?

Shawarata ga makaranta shi ne; su ringa uzuri ga marubuta domin marubuta mutanene tamkar kowa idan har an ga wani kuskure ko ajizanci a maimakon a aibata mutum ayi kokarin yi masa uzuri tare da nuna masa kuskurensa ta hanyar daya dace. Sannan makaranta su ringa karatu domin daukan darasin dake ciki ba iya zallar nishadi ba. Duk abin da marubuci ya kawo yana da dalilinsa da kuma abin da yake son isarwa amma sauda yawa makaranta sukan kulle idonsu su ki karbar gaskiya muddin ba ta zo daidai da ra’ayinsu ko abin da suka so ya kasance ba. Ga ‘yan’uwana marubuta kuma mu tsaya akan gaskiya, mu sani duk abin da muka rubuta akwai ranar da zamu tsaya gaban ubangiji akansa. Ina kira ga masu rubutun batsa da su ji tsoron Allah. Ko basu bari dan goben kansu da ta ‘ya’yansu ba domin duk wanda ya lalace sanadiyyar abin da suka rubutawa hakkinsa ba zai barsu ba ga tarin zunubi da suke daukarwa kansu da fushin ubangiji bisa yada barna a doron kasa. Mu yi rubutun da ko bayan ranmu za a karanta ayi mana addu’a. Mu yi rubutun da ba za mu ji kunyar nuna shi a ko ina ba. Da yawan marubutan batsa suna boye sunansu kenan sun san abin da suke aikatawa ba me kyau bane wadanda kuma suka shahara a ciki ba sa kunya ba kuma sa tsoron Allah suke yada badala da sunan neman kudi to su ji tsoron Allah domin rayuwar duniya ba matabbaciya ba ce fatan kowacce musulmi yayi karshe me kyau. Allah ya datar damu

 

Me za ki ce ga masu karanta labaranki?

Ina gaida masoya rubutuna duk inda kuke a fadin duniyar nan ina kuma Alfahari daku. SON SO FISABILLILLAH

 

Me za ki ce da makaranta shafin Adabi har ma da ita kanta jaridar LEADERSHIP?

Ina gaida duk wanda yake karanta wannan hira tawa idan ka/kin kasance me bibiyar littattafaina ina miki/maka albishir da labarai dake tafe wanda suka zarce na baya dadi da ma’ana. Ga wanda basu taba karanta littattafaina ba ku gwada ina da tabbacin ba za ku yi nadama ba. Jaridar leadership Hausa ina matukar godiya ga wannan dama da kuka ba ni. Ubangiji ya ci gaba da daukaka ku ya kuma kare mu baki daya daga dukkan abin ki. Nagode kwarai Allah ya saka muku da mafificin Alkhairi

 

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

Da farko ina gaida mahaifiyata ta Hajiya Ummu Usman, ina gaida maigidana Engineer A. Mainasara tare da yarana. Gaisuwar bangirma ga dukka masoyan rubutun Ummu-maheer musamman ‘yan groups dina na amana tun daga Rubutacciyar Kaddarah zuwa Wata kishiyar, Halin kishi da kuma Jama’ar Gidan BECHI kawayen Hajiya Binta da Afeeyah. Garkonin Ladies ko ince Shuwa Arabs kafataninku na gaishe ku musamman ‘yan aji uku Jaa, Ina gaida ‘yan’Uwana marubuta manya da yara tsofaffi da sababbi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Sana'o'in mataZamani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

Next Post

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Related

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

1 month ago
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

5 months ago
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya
Adabi

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

6 months ago
Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk
Adabi

Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk

7 months ago
Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad
Adabi

Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad

9 months ago
Marubuta Na Taimakawa Wajen Bunkasa Rayuwar Al’umma -Miyetti
Adabi

Marubuta Na Taimakawa Wajen Bunkasa Rayuwar Al’umma -Miyetti

9 months ago
Next Post
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

LABARAI MASU NASABA

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

June 2, 2025
2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

June 2, 2025
Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.