• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Yadda Ake Noman Albasa

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Albasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mafi yawan lokuta, ana yin girbin Albasa ne a cikin watan Nuwamba zuwa watan Disamba, sannan kuma tana kai wa tsawon watannin uku zuwa hudu kafin ta kai ga kamala girma baki-daya.

A daukacin fadin duniya, an yi matukar amincewa da Albasa sakamakon irin muhimmancin da take da shi, musamman a wajen hada abinci mai kara inganta lafi da dadi tare kuma da wasu abubuwa da take da su na daban.

Idan za ka shuka Albasa a cikin fili, ka shuka Irinta ya kai kimanin santi mita biyu, zurfin kuma ya kasance kimanin inci daya. Idan kuma za ka shuka Irin ne a layi, an son kakar sararin da ya kai daga kimanin santi mita talatin zuwa sama.

A wadane Jihohi Aka Fi Noman Albasa A Nijeriya?
An fi yin noman Albasa a Jihohin Kano, Kaduna, Jigawa, Sokkwato, Filato, Bauchi da kuma Kebbi, inda a shekarar 2012 kadai aka samar da kimanin Albasa wanda yawanta ya kai tan 240,000 na danyarta, inda kuma aka samar da tan 1,350,000 shi ma na bushasshiyarta.

Zuwa Tsawon Wane Lokaci Albasa Ke Girma Bayan Shuka Ta A Nijeriya?
Sakamakon yanayin zangon lokacin noma ta; har zuwa lokacin da ake yin girbinta tare da kuma adana ta, yana da matukar kyau ga masu noman wannan Albasa su tabbatar da sun yi matukar kiyayewa wajen zabo Irin shukar ta da ya fi da cewa tare kuma da inganci.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Mafi akasari daga kashi biyar zuwa takwas na Albasar da ake nomawa, ana yi ne a kakar sanyi; domin tana iya jurewa kowane irin yanayi, har ila yau akasari ana shinfida gadon da za a reni Irin Albasar, wanda zai kasance ya kai fadin mita daya, sannan kuma fadin dai ya kasance iya girman Lambu ko gonar da za a shuka Albasar, inda ake bukatar kula da wajen renon har zuwa kwana arba’in kafin a cire a kai zuwa wani sabon gurin daban.

Bayan kammala dukkanin gyare-gyare, sai a sake zuba su a cikin kedojen da za a shukata ko a tukwane, sannan kuma kasar noman da za a shuka ta ta kasance marar karfi, musamman domin jijiyoyinta su kara habaka da kuma saurin girma.

Albasa ta fi bukatar kasar noman da ke dauke da sinadaran gargajiya ko kuma sinadaran da ake kira a turance ‘Alkaline Acidic da kuma phosphate’, har Ila yau, an fi so a sake mata matsuguni da yamma bayan an yi mata ban ruwa, kazalika kuma; ana yi mata canjin waje daga tsawon santi mita 5 ko kuma daga tsawon santi mita 7.5.

Haka zalika, yana da matukar kyau a rika cire mata ciyawa bayan duk sati biyu tare kuma da yi mata ban ruwa sau biyu a duk sati, musamman a lokacin kakar sanyi ana bukatar ka yi mata feshi da nau’in maganin feshi mai inganci.

Bugu da kari, ana bukatar manomin Dawa ya dinga zuba mata takin zamani na NPK bayan ya canza mata wajen da zai shuka ta, haka nan Albasa na fara nuna ne daga bayan kwana 84 zuwa kwana 100 bayan an canza mata waje, idan kuma za a yi mata girbi, ana yi ne ta hanyar yin amfani da hannu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojojin Sin Da Amurka Sun Gana A Hawaii Don Tattauna Batun Tsaron Teku Da Na Sararin Sama

Next Post

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitulmalin Amurka A Guangzhou

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

6 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

6 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

6 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitulmalin Amurka A Guangzhou

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitulmalin Amurka A Guangzhou

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.