• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Yadda Ake Noman Albasa

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Albasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mafi yawan lokuta, ana yin girbin Albasa ne a cikin watan Nuwamba zuwa watan Disamba, sannan kuma tana kai wa tsawon watannin uku zuwa hudu kafin ta kai ga kamala girma baki-daya.

A daukacin fadin duniya, an yi matukar amincewa da Albasa sakamakon irin muhimmancin da take da shi, musamman a wajen hada abinci mai kara inganta lafi da dadi tare kuma da wasu abubuwa da take da su na daban.

Idan za ka shuka Albasa a cikin fili, ka shuka Irinta ya kai kimanin santi mita biyu, zurfin kuma ya kasance kimanin inci daya. Idan kuma za ka shuka Irin ne a layi, an son kakar sararin da ya kai daga kimanin santi mita talatin zuwa sama.

A wadane Jihohi Aka Fi Noman Albasa A Nijeriya?
An fi yin noman Albasa a Jihohin Kano, Kaduna, Jigawa, Sokkwato, Filato, Bauchi da kuma Kebbi, inda a shekarar 2012 kadai aka samar da kimanin Albasa wanda yawanta ya kai tan 240,000 na danyarta, inda kuma aka samar da tan 1,350,000 shi ma na bushasshiyarta.

Zuwa Tsawon Wane Lokaci Albasa Ke Girma Bayan Shuka Ta A Nijeriya?
Sakamakon yanayin zangon lokacin noma ta; har zuwa lokacin da ake yin girbinta tare da kuma adana ta, yana da matukar kyau ga masu noman wannan Albasa su tabbatar da sun yi matukar kiyayewa wajen zabo Irin shukar ta da ya fi da cewa tare kuma da inganci.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Mafi akasari daga kashi biyar zuwa takwas na Albasar da ake nomawa, ana yi ne a kakar sanyi; domin tana iya jurewa kowane irin yanayi, har ila yau akasari ana shinfida gadon da za a reni Irin Albasar, wanda zai kasance ya kai fadin mita daya, sannan kuma fadin dai ya kasance iya girman Lambu ko gonar da za a shuka Albasar, inda ake bukatar kula da wajen renon har zuwa kwana arba’in kafin a cire a kai zuwa wani sabon gurin daban.

Bayan kammala dukkanin gyare-gyare, sai a sake zuba su a cikin kedojen da za a shukata ko a tukwane, sannan kuma kasar noman da za a shuka ta ta kasance marar karfi, musamman domin jijiyoyinta su kara habaka da kuma saurin girma.

Albasa ta fi bukatar kasar noman da ke dauke da sinadaran gargajiya ko kuma sinadaran da ake kira a turance ‘Alkaline Acidic da kuma phosphate’, har Ila yau, an fi so a sake mata matsuguni da yamma bayan an yi mata ban ruwa, kazalika kuma; ana yi mata canjin waje daga tsawon santi mita 5 ko kuma daga tsawon santi mita 7.5.

Haka zalika, yana da matukar kyau a rika cire mata ciyawa bayan duk sati biyu tare kuma da yi mata ban ruwa sau biyu a duk sati, musamman a lokacin kakar sanyi ana bukatar ka yi mata feshi da nau’in maganin feshi mai inganci.

Bugu da kari, ana bukatar manomin Dawa ya dinga zuba mata takin zamani na NPK bayan ya canza mata wajen da zai shuka ta, haka nan Albasa na fara nuna ne daga bayan kwana 84 zuwa kwana 100 bayan an canza mata waje, idan kuma za a yi mata girbi, ana yi ne ta hanyar yin amfani da hannu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojojin Sin Da Amurka Sun Gana A Hawaii Don Tattauna Batun Tsaron Teku Da Na Sararin Sama

Next Post

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitulmalin Amurka A Guangzhou

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

4 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

5 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

5 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

6 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

2 weeks ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

2 weeks ago
Next Post
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitulmalin Amurka A Guangzhou

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitulmalin Amurka A Guangzhou

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.