ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Yadda Ake Noman Albasa

by Abubakar Abba
2 years ago
Albasa

Mafi yawan lokuta, ana yin girbin Albasa ne a cikin watan Nuwamba zuwa watan Disamba, sannan kuma tana kai wa tsawon watannin uku zuwa hudu kafin ta kai ga kamala girma baki-daya.

A daukacin fadin duniya, an yi matukar amincewa da Albasa sakamakon irin muhimmancin da take da shi, musamman a wajen hada abinci mai kara inganta lafi da dadi tare kuma da wasu abubuwa da take da su na daban.

Idan za ka shuka Albasa a cikin fili, ka shuka Irinta ya kai kimanin santi mita biyu, zurfin kuma ya kasance kimanin inci daya. Idan kuma za ka shuka Irin ne a layi, an son kakar sararin da ya kai daga kimanin santi mita talatin zuwa sama.

ADVERTISEMENT

A wadane Jihohi Aka Fi Noman Albasa A Nijeriya?
An fi yin noman Albasa a Jihohin Kano, Kaduna, Jigawa, Sokkwato, Filato, Bauchi da kuma Kebbi, inda a shekarar 2012 kadai aka samar da kimanin Albasa wanda yawanta ya kai tan 240,000 na danyarta, inda kuma aka samar da tan 1,350,000 shi ma na bushasshiyarta.

Zuwa Tsawon Wane Lokaci Albasa Ke Girma Bayan Shuka Ta A Nijeriya?
Sakamakon yanayin zangon lokacin noma ta; har zuwa lokacin da ake yin girbinta tare da kuma adana ta, yana da matukar kyau ga masu noman wannan Albasa su tabbatar da sun yi matukar kiyayewa wajen zabo Irin shukar ta da ya fi da cewa tare kuma da inganci.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Mafi akasari daga kashi biyar zuwa takwas na Albasar da ake nomawa, ana yi ne a kakar sanyi; domin tana iya jurewa kowane irin yanayi, har ila yau akasari ana shinfida gadon da za a reni Irin Albasar, wanda zai kasance ya kai fadin mita daya, sannan kuma fadin dai ya kasance iya girman Lambu ko gonar da za a shuka Albasar, inda ake bukatar kula da wajen renon har zuwa kwana arba’in kafin a cire a kai zuwa wani sabon gurin daban.

Bayan kammala dukkanin gyare-gyare, sai a sake zuba su a cikin kedojen da za a shukata ko a tukwane, sannan kuma kasar noman da za a shuka ta ta kasance marar karfi, musamman domin jijiyoyinta su kara habaka da kuma saurin girma.

Albasa ta fi bukatar kasar noman da ke dauke da sinadaran gargajiya ko kuma sinadaran da ake kira a turance ‘Alkaline Acidic da kuma phosphate’, har Ila yau, an fi so a sake mata matsuguni da yamma bayan an yi mata ban ruwa, kazalika kuma; ana yi mata canjin waje daga tsawon santi mita 5 ko kuma daga tsawon santi mita 7.5.

Haka zalika, yana da matukar kyau a rika cire mata ciyawa bayan duk sati biyu tare kuma da yi mata ban ruwa sau biyu a duk sati, musamman a lokacin kakar sanyi ana bukatar ka yi mata feshi da nau’in maganin feshi mai inganci.

Bugu da kari, ana bukatar manomin Dawa ya dinga zuba mata takin zamani na NPK bayan ya canza mata wajen da zai shuka ta, haka nan Albasa na fara nuna ne daga bayan kwana 84 zuwa kwana 100 bayan an canza mata waje, idan kuma za a yi mata girbi, ana yi ne ta hanyar yin amfani da hannu.

Albasa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitulmalin Amurka A Guangzhou

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitulmalin Amurka A Guangzhou

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.