• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijar: Sojoji Sun Kame Manyan ‘Yan Siyasa Da Ministocin Bazoum 

by Sadiq
2 years ago
Nijar

Rahotannin da ke fitowa daga Jamhuriyar Nijar na nuni da cewa gwamnatin mulkin soja a kasar ta fara kame jami’an gwamnati da suka hada da ministan ma’adinai na jam’iyya mai mulki, da kuma ministan mai Mahamane Mahamadou, wanda kuma dan tsohon shugaban kasar, Issoufou Mahamadou ne.

Ministoci akalla hudu ne da suka hada da tsohon minista da kuma shugaban jam’iyyar hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum ne, aka kama a hannun gwamnatin soja da ta kwace mulki a ranar 26 ga watan Yuli, in ji jam’iyyar a ranar Litinin.

  • Ba Abin Da Zai Hana Mu Shiga Zanga-Zanga —NLC
  • A Guji Tarzoma Yayin Zanga-zanga, IGP Ya Gargadi NLC Da TUC

“Bayan an tsare shugaban kasar a makon da ya gabata, sojojin sun sake tsare wasu,” in ji jam’iyyar Democratic Democratic Party (PNDS) a cikin wata sanarwa.

“A safiyar ranar Litinin, an kama ministan mai, Mahamane Sani Mahamadou, dan tsohon shugaban kasa Mahamadou Issoufou da kuma ministan ma’adinai Ousseini Hadizatou,” in ji sanarwar.

An kuma kama shugaban kwamitin zartarwa na PNDS na kasa, Fourmakoye Gado, in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

A baya dai gwamnatin mulkin sojan kasar ta kama ministan harkokin cikin gida Hama Amadou Souley da ministan sufuri Oumarou Malam Alma da kuma Kalla Moutari dan majalisa kuma tsohon ministan tsaro, in ji jam’iyyar.

Jam’iyyar ta yi kira da a sake su cikin gaggawa, tana mai cewa Nijar na cikin tsaka mai wuya.

Wata majiya da ke kusa da fadar shugaban kasar ta ce an kuma kama ministan koyar da sana’o’i, Kassoum Moctar.

Kamen ya zo daidai da wata sanarwa da gwamnatin mulkin sojan kasar ta bayar na bukatar “dukkan tsofaffin ministoci da shugabannin hukumomi da su mika motocin ofishinsu.

A ranar Larabar da ta gabata ne wasu jami’an tsaron fadar shugaban kasar suka hambarar da gwamnatin shugaba Bazoum, wanda shugabansu Abdourahamane Tiani, ya ayyana kansa a matsayin sabon shugaban kasar.

Sai dai ECOWAS da Majalisar Dinkin Duniya sun yi Allah-wadai da juyin mulki da sojojin suka yi.

Inda suka ba su wa’adin mako guda don dawo da mulki ga shugaba Bazoum.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu
Manyan Labarai

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato
Manyan Labarai

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
Manyan Labarai

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Next Post
Barcelona Ta Doke AC Milan A Wasan Sada Zumunta

Barcelona Ta Doke AC Milan A Wasan Sada Zumunta

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.