• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijar: Sojoji Sun Kame Manyan ‘Yan Siyasa Da Ministocin Bazoum 

by Sadiq
2 years ago
Nijar

Rahotannin da ke fitowa daga Jamhuriyar Nijar na nuni da cewa gwamnatin mulkin soja a kasar ta fara kame jami’an gwamnati da suka hada da ministan ma’adinai na jam’iyya mai mulki, da kuma ministan mai Mahamane Mahamadou, wanda kuma dan tsohon shugaban kasar, Issoufou Mahamadou ne.

Ministoci akalla hudu ne da suka hada da tsohon minista da kuma shugaban jam’iyyar hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum ne, aka kama a hannun gwamnatin soja da ta kwace mulki a ranar 26 ga watan Yuli, in ji jam’iyyar a ranar Litinin.

  • Ba Abin Da Zai Hana Mu Shiga Zanga-Zanga —NLC
  • A Guji Tarzoma Yayin Zanga-zanga, IGP Ya Gargadi NLC Da TUC

“Bayan an tsare shugaban kasar a makon da ya gabata, sojojin sun sake tsare wasu,” in ji jam’iyyar Democratic Democratic Party (PNDS) a cikin wata sanarwa.

“A safiyar ranar Litinin, an kama ministan mai, Mahamane Sani Mahamadou, dan tsohon shugaban kasa Mahamadou Issoufou da kuma ministan ma’adinai Ousseini Hadizatou,” in ji sanarwar.

An kuma kama shugaban kwamitin zartarwa na PNDS na kasa, Fourmakoye Gado, in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

A baya dai gwamnatin mulkin sojan kasar ta kama ministan harkokin cikin gida Hama Amadou Souley da ministan sufuri Oumarou Malam Alma da kuma Kalla Moutari dan majalisa kuma tsohon ministan tsaro, in ji jam’iyyar.

Jam’iyyar ta yi kira da a sake su cikin gaggawa, tana mai cewa Nijar na cikin tsaka mai wuya.

Wata majiya da ke kusa da fadar shugaban kasar ta ce an kuma kama ministan koyar da sana’o’i, Kassoum Moctar.

Kamen ya zo daidai da wata sanarwa da gwamnatin mulkin sojan kasar ta bayar na bukatar “dukkan tsofaffin ministoci da shugabannin hukumomi da su mika motocin ofishinsu.

A ranar Larabar da ta gabata ne wasu jami’an tsaron fadar shugaban kasar suka hambarar da gwamnatin shugaba Bazoum, wanda shugabansu Abdourahamane Tiani, ya ayyana kansa a matsayin sabon shugaban kasar.

Sai dai ECOWAS da Majalisar Dinkin Duniya sun yi Allah-wadai da juyin mulki da sojojin suka yi.

Inda suka ba su wa’adin mako guda don dawo da mulki ga shugaba Bazoum.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Next Post
Barcelona Ta Doke AC Milan A Wasan Sada Zumunta

Barcelona Ta Doke AC Milan A Wasan Sada Zumunta

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.