• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Amurka Sun Jaddada Kudurin Karfafa Kasuwanci A Tsakaninsu

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Nijeriya Da Amurka Sun Jaddada Kudurin Karfafa Kasuwanci A Tsakaninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin yanzu Nijeriya da kasar Amurka sun jaddada shirin kara karfafa harkokin kasuwanci da zuba jari a tsakaninsu.

 

Wannann ya biyo bayan taron koli nena kasashen da ya gudana a tsakanin Ministar Masa’anatu, Kasuwanci da Zuba Jari na Nijeriya, Dakta Doris Uzoka-Anite, da tawagar kasar Amurka a karkashin jagorancin mataimakin sakatare mai kula da harkokin ciniki da kasuwanci tsakanin kasashen waje, Mista Arun Benkataraman, a Abuja ranar Laraba.

  • Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Na Shirin Shiriricewa
  • Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Kan Zanga-zangar Matsin Rayuwa

Taron ya mayar da hankali ne wajen karfafawa tare da tabbatar da yarjejeniyar da ke tsakanin kasashen biyu da suka hada da shirin nan na (TIFA) da (AGOA) da (BNC) da kuma (CID) wadanda ke karfafa kasuwanci a tsakanin kasashen Afrika da duniya baki daya ba a manta da su ba.

 

Labarai Masu Nasaba

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

Duka bangarorin sun karfafa bukatar fadada harkokin kasuwanci a tsakaninsu tare da kuma kirkiro da sabbin hanyoyin cimma bukatun kasashen nasu domin bunkasa tattalin arzikin juna.

 

Dakta Uzoka-Anite ta bayyana abubuwan da Amurka za ta amfana dasu a Nijeriya wadanda suka hada da kasancewar ta babbar kasuwar da babu irinta a nan kusa da kuma ma’adanai da Allah ya hore mana a sassan kasa, haka kuma muna da kwararru masu ilimi daban-daban da za a iya fitar dasu zuwa kasashen waje su amfanar da kasashe daban-daban,” in ji ta.

 

Ta kuma jinjina wa dangantakar da ke tsakanin Nijeriya da Amurka. “Nijeriya da Amurka sun dade suna hulda da juna na tsawon shekaru, suna mutunta juna tare da amfanar juna a bangarorin tattalin arziki da dama,” in ji ta.

 

A nasa jawabin, Benkataraman ya sanar da goyon bayan Amurka ga shirin farfado da tattalin arzikn kasa da kuma irin kalubalen da kamfanonin Amurka da ke harkoki a Nijeriya ke fuskanta.

 

“Za mu yi aiki domin karfafa dangantakar da ke tsakanin mu domin samun ci gaba da bunkasar tattalin arziki ta yadda al’ummar kasashen biyu za su amfana,” in ji shi.

 

Tawagar ta kasa Amurka ta nuna sha’awarta ga sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Tinubu take yi, sun kuma yi alkawarin bayar da gudummawarsu wajen karfafa kasuwanci da zuba jari a Nijeriya a daidai wannan lokacin.

 

Duka bangarorin sun amince da ci gaba da tattaunawa akai akai tsakaninsu don tabbatar da dorewar yarjejeniyar da aka kulla. An kammala taron tare da alkawarin kara karfafa kasuwanci da zuba jari a tsakanin kasashen biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Afirka da AmurkaBunkasa Tattalin ArzikiGwamnatin Tarayya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Juma’a

Next Post

Jami’ar Bayero Ta Fito Da Kurakuran Da Ake Tafkawa A Rediyo Da Talabijin

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

2 days ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

1 week ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

2 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

2 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

3 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

4 weeks ago
Next Post
BUK

Jami’ar Bayero Ta Fito Da Kurakuran Da Ake Tafkawa A Rediyo Da Talabijin

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.