• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Fuskantar Karancin Alkalai

by Leadership Hausa
2 years ago
in Rahotonni
0
Alkalai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayanan da aka samu a ‘yan kwanakin nan na nuna akwai karancin alkalai da mayan ma’aikata musamman a manyan kotuna kassar nan, Kotun Koli da Kotun Daukaka Kara.

Rahotanni sun bayyana cewa, karancin alkalai a Kotun Koli ya bayyana ne bayan ajiye aikin da Maishari’a Amina Adamu Augie, da Maishari’a Mary Odili wadda ta yi ritaya kafin ita da kuma rasuwar Maishari’a Centus Chima Nweze. Rahoton ya kuma nuna cewa, a halin yanzu alkalai 11 suka rage maimakon alkalai 21 da doka ta tanada. Wannan lamarin yana matukar nakasa ayyukan masu shari’a saboda yawan aikin da ke gaban su hakan kuma yana shafar kokarin su na sauke nauyin yanke hukunce-hukunce a shari’un da ke gaban su.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Agaji Bayan Da Ya Kai Musu Kudin Fansa A Kaduna
  • Jirgin Sojoji Ya Yi Wa ‘Yan Ta’adda Luguden Wuta A Zamfara

Karin matsalar kuma a nan shi ne a cikin alkalai 11 da suka rare a kotun kolin 7 daga cikin su za su shiga aikin sauraran daukaka karar da da ‘yan takarar shugabancin kasar nan Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP da Peter Obi na jam’iyyar LP sai kuma jam’iyya APM wadanda suke kalubalantar nasarar da dan takarar jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu a zaben da aka yi a shekarar 2023 wanda kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa ta tabbatar masa da nasara kwanakin baya.

Haka ya zama saura alkalai 4 kenan da za su fuskanci dinbin kararrakin da ke gaban Koton Kolin ciki har da kararrakin zaben gwamnoni wanda shi ma sai ya dangana da Koton Koli don yanke hukunci.

Hukumar Kula da Harkokin Shari’a (NJC) ce ke da alhakin amincewa da wadanda za a nada a matsayin alkalai a Koton Kolin daga na sai shugaban kasa ya mika sunayen su ga majalisar dattawa don su tabbatar da su, aikin su ne yanke hukunci a kan matsalolin da sukan taso a tsakanin gwamnatin tarayya da na jihohi da kuma matsalolin da ke tasowa a tsakanin jiha da jiha da sauran rikice-rikice a tsakanin al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

Shugabanin manyan kotuna biyu na kasa sun koka a kan yadda aiki ya yi musu yawa da kuma karancin alkalai da za su fuskanci ayyukan. A jawabinsa kwanakin baya lokacin da ake rantsar da alkalai 9 da za su yi aiki a kotun daukaka kara, alkalain alkalan Nijeriya, Maishari’a Olukayode Ariwoola, ya koka a kan yadda shari’un zabe suka cika kotunanmu, ya ce, suna matukar takura alkalai, aikin kuma yana yi musu yawa kwarai da gaske, in ji shi.

A watan Nuwamba na shekarar da ta gabata, a yayin rantsar da sabbin manyan lauyoyi 62 na kasa a Abuja, alkalin alkalan Nijeriya Ariwoola ya jaddada cewa, bincdike ya nuna cewa Koton Kolin Nijeriya ce tafi duk wata kotun koli a duniya yawan ayyuka, wanan yana nuna irin aiki tukurun manyan alkalan Nijeriya.

A yayin da ake shari’u fiye da 6,884 kuma gashi alkalan da za su saurari wadanna shari’un suna kara raguwa, lallai za a iya samun matsalar dadewa shari’u, wanda kuma dadewar shari’a tamkar rashin aldalci ne ga masu neman hakkinsu.

Rahotanni sun nuna cewa a bayan zaben shekarar 2023 manyan kotunan tarayya sun karbi kararraki fiye da 3,000 wadanda ake sa ran za su bi ta kutunnan daukaka kara har zuwa Koton Koli don warwarewa.

Haka kuma shugabar kotun daukaka kara, Mai shari’a Dongban-Mensem, ta yi bayani kamar yadda alkalin alkalan Nijeriya ya yi a yayin kaddamar da shekarar shari’a ta 2023/2024.

Ta ce, kutun na da kararraki fiye da 39,526 wadanda suka rarraba a bangarorin kotun 20 sun kuma hada da kararrakin zabe. Maishari’a Dongban-Mensem ta bayyana cewa, bayan babban zaben 2023 sun kafa kotunan zabe 98 da za su duba shari’u 1,209 da ‘yan takarar zabe suka mika wa kotunan a jihohi daban daban.

Ta bayyana damuwar ta a kan yadda shari’un zabe suka cika kotunan Nijeriya wanda hakan na nufin cewa, sauran matsaloli da suka shafi rikice-rikicen filaye, hakokin dan adam, matsalar kasuwanci da sauran rikice-rikice za su ci gaba da zama a kotuna na tsawon lokaci.

Alkali alkalan Nijeriya, Ariwoola da shugabar kotun daukaka kara, Dongban-Mensen sun yi kira da cewa, bai kamata a ce dukkan shari’un zabe sai sun dangana ga kotuna ba, ya kamata a rinka neman hanyar warware rikice -rikicen zabe musamman ganin yadda kotuna suka cika da shari’u da ke bukatar a funskance su a kotunanmu.

Yana kuma da matukar muhimmanci a a kafa kotuna na musamman don sauraron kararrakin zabe kamar yadda kungiyar lauyoyi ta kasa ta yi kwanakin baya, a kan haka kuma muna kira ga Hukumar Kula da Harkokin Shari’a NJC ta mika sunayen wadanda ya kamata a nada a mastayin alkalan Koton Koli kamar yadda dokar kasa ta 230(1) (B) na kundin tsarin mulkin Nijeriya ya samar, ya kuma kamata a samar da isassun ma’aikata a kananan kotunan kasar nan don aiki a kan shari’un da ke gabansu kamar yadda ya kamata, kuma kan lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alkalin AlkalaiKotunan NijeriyaShari'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Minista Alhaji Bello Maitama Yusuf Ya Rasu Yana Da Shekaru 76 A Kano

Next Post

Tsoron Allah Da Ibadar Annabi (SAW)

Related

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

4 days ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

5 days ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

7 days ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

2 weeks ago
Next Post
Maulid

Tsoron Allah Da Ibadar Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.