• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Ƙarfafa Alaƙa Da Indonesiya A Taron Ƙasar Da  Ƙasashen Afirka Karo Na Biyu

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Nijeriya Za Ta Ƙarfafa Alaƙa Da Indonesiya A Taron Ƙasar Da  Ƙasashen Afirka Karo Na Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Nijeriya za ta ƙarfafa hulɗar da ke tsakanin ta da Indonesiya yayin da aka fara taron ƙasar da nahiyar Afirka karo na biyu a birnin Bali na ƙasar Indonesiya.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan, wanda yanzu haka yake Indonesiya domin wakiltar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a matsayin Shugaban Tawagar Nijeriya a taron.

  • ACF Ta Yaba Wa Tinubu Kan Amincewa Da Ziyarar Sulhu Da Shugaban Sojojin Nijeriya Ya Kai A Nijar 
  • Masanin Habasha: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Jure Sauye Sauye Cikin Tsawon Lokaci

Taron zai gudana ne daga ranar 1 zuwa 3 ga Satumba, 2024.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

Taken taron, “Bandung Spirit for Africa’s Agenda 2023” kwatankwacin taron Asiya da Afirka ne mai tarihi na 1955 da aka fi sani da “Taron Bandung”, wanda Indonesiya ta shirya, wanda ya nuna wani sabon babi na haɗin kai da haɗin gwiwa a cikin alakar da ke tsakanin nahiyoyin biyu.

 

Taken, kuma yana da nufin zurfafa haɗin gwiwa tsakanin Muradin Indonesiya na 2045 da Ajandar Tarayyar Afirka ta 2063.

 

Nijeriya da Indonesiya dai suna da alaƙa mai ƙarfi tsawon shekaru, wanda tun a shekarar 2022 gwamnatin Indonesiya ta ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da za ta zuba jari a cikin ta a nahiyar Afirka, matakin da ke nuna amincewar ƙasar da ƙarfin tattalin arzikin Nijeriya.

 

Adadin cinikayyar da ke tsakanin ƙasashen biyu ya kai dala biliyan 6 a 2023, wanda ya ƙaru daga dala biliyan 4 shekaru goma da suka gabata.

 

Bugu da ƙari, tallafin da Indonesiya ta bai wa Nijeriya ya haɗa da ba da gudunmawa a 2023 ta allurar rigakafi ta Pentavalent miliyan 1.58, wadda darajar ta ta kai kusan dalar Amurka miliyan 2, wanda ya kasance muhimmi wajen kare yaran Nijeriya daga cututtuka masu barazana ga rayuwa.

 

Yayin da yake Indonesiya, Minista Idris zai bayyana damarmakin saka hannun jari a Nijeriya a ɓangarori daban-daban da kuma bayyana nasarorin da aka samu na zamantakewa da tattalin arziki na Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Tinubu.

 

Zai kuma nemi a bai wa ‘yan kasuwa na Nijeriya damarmakin da za su shiga cikin tattalin arzikin Indonesiya.

 

“Ina fatan in wakilci Mai Girma Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da gwamnati da al’ummar Nijeriya a taron Indonesiya da Afirka karo na biyu, da kuma taron da zai zama wani muhimmin abin tunawa a cikin tafiyar ƙarfafa alaƙa tsakanin Indonesiya a ɓangare ɗaya da Nijeriya da Afirka a ɗaya ɓangaren,” inji Idris.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Nijeriya da TuraiKasashen duniyaZuba Jari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Kebbi Ya Rantsar Da Zaɓaɓɓun Shugabannin Ƙananan Hukumomi

Next Post

Sojoji Sun Kama Masu Safarar Makamai Ga Ƴan Ta’adda

Related

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

56 seconds ago
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku
Labarai

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

41 minutes ago
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 
Labarai

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

1 hour ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

5 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

6 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

19 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kama Masu Safarar Makamai Ga Ƴan Ta’adda

Sojoji Sun Kama Masu Safarar Makamai Ga Ƴan Ta'adda

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.