ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Ƙarfafa Alaƙa Da Indonesiya A Taron Ƙasar Da  Ƙasashen Afirka Karo Na Biyu

by Sulaiman
2 years ago
Indonesiya

Gwamnatin Nijeriya za ta ƙarfafa hulɗar da ke tsakanin ta da Indonesiya yayin da aka fara taron ƙasar da nahiyar Afirka karo na biyu a birnin Bali na ƙasar Indonesiya.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan, wanda yanzu haka yake Indonesiya domin wakiltar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a matsayin Shugaban Tawagar Nijeriya a taron.

ADVERTISEMENT
  • ACF Ta Yaba Wa Tinubu Kan Amincewa Da Ziyarar Sulhu Da Shugaban Sojojin Nijeriya Ya Kai A Nijar 
  • Masanin Habasha: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Jure Sauye Sauye Cikin Tsawon Lokaci

Taron zai gudana ne daga ranar 1 zuwa 3 ga Satumba, 2024.

 

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Taken taron, “Bandung Spirit for Africa’s Agenda 2023” kwatankwacin taron Asiya da Afirka ne mai tarihi na 1955 da aka fi sani da “Taron Bandung”, wanda Indonesiya ta shirya, wanda ya nuna wani sabon babi na haɗin kai da haɗin gwiwa a cikin alakar da ke tsakanin nahiyoyin biyu.

 

Taken, kuma yana da nufin zurfafa haɗin gwiwa tsakanin Muradin Indonesiya na 2045 da Ajandar Tarayyar Afirka ta 2063.

 

Nijeriya da Indonesiya dai suna da alaƙa mai ƙarfi tsawon shekaru, wanda tun a shekarar 2022 gwamnatin Indonesiya ta ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da za ta zuba jari a cikin ta a nahiyar Afirka, matakin da ke nuna amincewar ƙasar da ƙarfin tattalin arzikin Nijeriya.

 

Adadin cinikayyar da ke tsakanin ƙasashen biyu ya kai dala biliyan 6 a 2023, wanda ya ƙaru daga dala biliyan 4 shekaru goma da suka gabata.

 

Bugu da ƙari, tallafin da Indonesiya ta bai wa Nijeriya ya haɗa da ba da gudunmawa a 2023 ta allurar rigakafi ta Pentavalent miliyan 1.58, wadda darajar ta ta kai kusan dalar Amurka miliyan 2, wanda ya kasance muhimmi wajen kare yaran Nijeriya daga cututtuka masu barazana ga rayuwa.

 

Yayin da yake Indonesiya, Minista Idris zai bayyana damarmakin saka hannun jari a Nijeriya a ɓangarori daban-daban da kuma bayyana nasarorin da aka samu na zamantakewa da tattalin arziki na Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Tinubu.

 

Zai kuma nemi a bai wa ‘yan kasuwa na Nijeriya damarmakin da za su shiga cikin tattalin arzikin Indonesiya.

 

“Ina fatan in wakilci Mai Girma Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da gwamnati da al’ummar Nijeriya a taron Indonesiya da Afirka karo na biyu, da kuma taron da zai zama wani muhimmin abin tunawa a cikin tafiyar ƙarfafa alaƙa tsakanin Indonesiya a ɓangare ɗaya da Nijeriya da Afirka a ɗaya ɓangaren,” inji Idris.

Indonesiya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kama Masu Safarar Makamai Ga Ƴan Ta’adda

Sojoji Sun Kama Masu Safarar Makamai Ga Ƴan Ta'adda

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.