ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Ƙarfafa Alaƙa Da Indonesiya A Taron Ƙasar Da  Ƙasashen Afirka Karo Na Biyu

by Sulaiman
2 years ago
Indonesiya

Gwamnatin Nijeriya za ta ƙarfafa hulɗar da ke tsakanin ta da Indonesiya yayin da aka fara taron ƙasar da nahiyar Afirka karo na biyu a birnin Bali na ƙasar Indonesiya.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan, wanda yanzu haka yake Indonesiya domin wakiltar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a matsayin Shugaban Tawagar Nijeriya a taron.

ADVERTISEMENT
  • ACF Ta Yaba Wa Tinubu Kan Amincewa Da Ziyarar Sulhu Da Shugaban Sojojin Nijeriya Ya Kai A Nijar 
  • Masanin Habasha: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Jure Sauye Sauye Cikin Tsawon Lokaci

Taron zai gudana ne daga ranar 1 zuwa 3 ga Satumba, 2024.

 

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Taken taron, “Bandung Spirit for Africa’s Agenda 2023” kwatankwacin taron Asiya da Afirka ne mai tarihi na 1955 da aka fi sani da “Taron Bandung”, wanda Indonesiya ta shirya, wanda ya nuna wani sabon babi na haɗin kai da haɗin gwiwa a cikin alakar da ke tsakanin nahiyoyin biyu.

 

Taken, kuma yana da nufin zurfafa haɗin gwiwa tsakanin Muradin Indonesiya na 2045 da Ajandar Tarayyar Afirka ta 2063.

 

Nijeriya da Indonesiya dai suna da alaƙa mai ƙarfi tsawon shekaru, wanda tun a shekarar 2022 gwamnatin Indonesiya ta ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da za ta zuba jari a cikin ta a nahiyar Afirka, matakin da ke nuna amincewar ƙasar da ƙarfin tattalin arzikin Nijeriya.

 

Adadin cinikayyar da ke tsakanin ƙasashen biyu ya kai dala biliyan 6 a 2023, wanda ya ƙaru daga dala biliyan 4 shekaru goma da suka gabata.

 

Bugu da ƙari, tallafin da Indonesiya ta bai wa Nijeriya ya haɗa da ba da gudunmawa a 2023 ta allurar rigakafi ta Pentavalent miliyan 1.58, wadda darajar ta ta kai kusan dalar Amurka miliyan 2, wanda ya kasance muhimmi wajen kare yaran Nijeriya daga cututtuka masu barazana ga rayuwa.

 

Yayin da yake Indonesiya, Minista Idris zai bayyana damarmakin saka hannun jari a Nijeriya a ɓangarori daban-daban da kuma bayyana nasarorin da aka samu na zamantakewa da tattalin arziki na Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Tinubu.

 

Zai kuma nemi a bai wa ‘yan kasuwa na Nijeriya damarmakin da za su shiga cikin tattalin arzikin Indonesiya.

 

“Ina fatan in wakilci Mai Girma Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da gwamnati da al’ummar Nijeriya a taron Indonesiya da Afirka karo na biyu, da kuma taron da zai zama wani muhimmin abin tunawa a cikin tafiyar ƙarfafa alaƙa tsakanin Indonesiya a ɓangare ɗaya da Nijeriya da Afirka a ɗaya ɓangaren,” inji Idris.

Indonesiya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • Sulaiman
    Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman
  • Sulaiman
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya
Labarai

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kama Masu Safarar Makamai Ga Ƴan Ta’adda

Sojoji Sun Kama Masu Safarar Makamai Ga Ƴan Ta'adda

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.