• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Zuba Tiriliyan 2 Don Bunkasa Tattalin Arziki

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Bola Tinubu ya shirya wani yunkurin bunkasa tattalin arziki da ya kai Naira tiliyan 2 daidai da dala biliyan 1.3 don magance manyan matsaloli, ciki har da samar da abinci.

Tinubu ya umarci tawagarsa ta tattalin arziki su shirya wani tsari na zuba Naira tiriliyan biyu, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 1.33 don magance matsalolin da ake da su game da samar da abinci da hauhauwar farashi da kuma karfafa muhimman sassa, in ji Ministan Kudi a ranar Alhamis.

  • Binciken CGTN: Kusan Kashi 90 Cikin Dari Sun Goyi Bayan Habaka Hadin Gwiwar Inganta Aikin AI
  • Binciken Ganduje: Kotu Ta Bai Wa Alkalan Kano Sa’o’i 48 Su Yi Murabus

Shirin, wanda za a aiwatar da shi tare da hadin gwiwar gwamnatocin jihohi da kamfanoni masu zaman kansu, zai ware naira tiriliyan daya, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 664.45 ga harkokin noma da samar da abinci da kuma bangaren makamashi, sai wata Naira biliyan 350 domin kula da lafiya da walwalar jama’a, kamar yadda Olawale Edun ya fada wa manema labarai.

Tun bayan hawansa mulki a watan Mayun bara, Tinubu ya aiwatar da sauye-sauye da suka haɗa da rage tallafin man fetur da wutar lantarki da kuma rage darajar Naira sau biyu, a yayin da yake fafutukar kara zuba jari da kara yawan kayayyakin da ake samarwa.

Sai dai tattalin arzikin kasar ba ya samun ci gaba cikin sauri kasa da 6% a duk shekara kamar yadda ya yi fata, yayin da sauye-sauyen suka sa tashin farashin kayayyaki ya kai mafi muni a cikin shekara 28, ya kuma ta’azzara yanayin rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Samar da abinci

“Abu na farko da shugaban ya mayar da hankali a kai shi ne samar da abinci” a cewar Edun ranar Laraba bayan da Tinubu ya kaddamar da wani gyara na tsarin tafiyar da tattalin arziki.

Edun ya ce “Jajircewa wajen samar da abinci a farashi mai rahusa da kuma samar da shi da yawa shi ne abin da Shugaban Ƙasa ya fi mayar da hankali a wannan lokaci.”

Har ila yau, shirin na son magance matsalar raguwar yawan man da ake hakowa da nufin ƙara yawansa zuwa ganga miliyan biyu a kowace rana, ta yadda za a samar da ƙarin kudaden shiga da kuma musayar kudaden waje ga tattalin arzikin kasar.

Nijeriya ta dogara ne da man fetur wajen samun fiye da rabin kudaden shigarta da kuma kusan kashi 90% na kudin waje.

Sai dai yawan man da ake hakowa ya ragu a shekarun baya-bayan nan, inda satar man da zagon kasa da kuma ficewar manyan kamfanoni daga wuraren da ake haƙo man saboda matsalar rashin tsaro, inda suke mayar da hankali kan binciken mai a teku.

Edun bai fayyace lokacin aiwatar da shirin bunƙasa tattalin arzikin ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiTattalin ArzikiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Binciken CGTN: Kusan Kashi 90 Cikin Dari Sun Goyi Bayan Habaka Hadin Gwiwar Inganta Aikin AI

Next Post

Matsalar ‘Yan sandan Amurka Ta Nuna Karfin Tuwo Na Kara Tsananta

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

6 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

6 hours ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

17 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

18 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

1 day ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

1 day ago
Next Post
Matsalar ‘Yan sandan Amurka Ta Nuna Karfin Tuwo Na Kara Tsananta

Matsalar ‘Yan sandan Amurka Ta Nuna Karfin Tuwo Na Kara Tsananta

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Bunkasa

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.