• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Zuba Tiriliyan 2 Don Bunkasa Tattalin Arziki

by Sadiq
12 months ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Bola Tinubu ya shirya wani yunkurin bunkasa tattalin arziki da ya kai Naira tiliyan 2 daidai da dala biliyan 1.3 don magance manyan matsaloli, ciki har da samar da abinci.

Tinubu ya umarci tawagarsa ta tattalin arziki su shirya wani tsari na zuba Naira tiriliyan biyu, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 1.33 don magance matsalolin da ake da su game da samar da abinci da hauhauwar farashi da kuma karfafa muhimman sassa, in ji Ministan Kudi a ranar Alhamis.

  • Binciken CGTN: Kusan Kashi 90 Cikin Dari Sun Goyi Bayan Habaka Hadin Gwiwar Inganta Aikin AI
  • Binciken Ganduje: Kotu Ta Bai Wa Alkalan Kano Sa’o’i 48 Su Yi Murabus

Shirin, wanda za a aiwatar da shi tare da hadin gwiwar gwamnatocin jihohi da kamfanoni masu zaman kansu, zai ware naira tiriliyan daya, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 664.45 ga harkokin noma da samar da abinci da kuma bangaren makamashi, sai wata Naira biliyan 350 domin kula da lafiya da walwalar jama’a, kamar yadda Olawale Edun ya fada wa manema labarai.

Tun bayan hawansa mulki a watan Mayun bara, Tinubu ya aiwatar da sauye-sauye da suka haɗa da rage tallafin man fetur da wutar lantarki da kuma rage darajar Naira sau biyu, a yayin da yake fafutukar kara zuba jari da kara yawan kayayyakin da ake samarwa.

Sai dai tattalin arzikin kasar ba ya samun ci gaba cikin sauri kasa da 6% a duk shekara kamar yadda ya yi fata, yayin da sauye-sauyen suka sa tashin farashin kayayyaki ya kai mafi muni a cikin shekara 28, ya kuma ta’azzara yanayin rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Samar da abinci

“Abu na farko da shugaban ya mayar da hankali a kai shi ne samar da abinci” a cewar Edun ranar Laraba bayan da Tinubu ya kaddamar da wani gyara na tsarin tafiyar da tattalin arziki.

Edun ya ce “Jajircewa wajen samar da abinci a farashi mai rahusa da kuma samar da shi da yawa shi ne abin da Shugaban Ƙasa ya fi mayar da hankali a wannan lokaci.”

Har ila yau, shirin na son magance matsalar raguwar yawan man da ake hakowa da nufin ƙara yawansa zuwa ganga miliyan biyu a kowace rana, ta yadda za a samar da ƙarin kudaden shiga da kuma musayar kudaden waje ga tattalin arzikin kasar.

Nijeriya ta dogara ne da man fetur wajen samun fiye da rabin kudaden shigarta da kuma kusan kashi 90% na kudin waje.

Sai dai yawan man da ake hakowa ya ragu a shekarun baya-bayan nan, inda satar man da zagon kasa da kuma ficewar manyan kamfanoni daga wuraren da ake haƙo man saboda matsalar rashin tsaro, inda suke mayar da hankali kan binciken mai a teku.

Edun bai fayyace lokacin aiwatar da shirin bunƙasa tattalin arzikin ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiTattalin ArzikiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Binciken CGTN: Kusan Kashi 90 Cikin Dari Sun Goyi Bayan Habaka Hadin Gwiwar Inganta Aikin AI

Next Post

Matsalar ‘Yan sandan Amurka Ta Nuna Karfin Tuwo Na Kara Tsananta

Related

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

10 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

15 hours ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

19 hours ago
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

21 hours ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

22 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

1 day ago
Next Post
Matsalar ‘Yan sandan Amurka Ta Nuna Karfin Tuwo Na Kara Tsananta

Matsalar ‘Yan sandan Amurka Ta Nuna Karfin Tuwo Na Kara Tsananta

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.