ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku Kan Sabon Yajin Aiki Da ASUU Ta Tsunduma

by Aisha Seyoji
4 years ago
ASUU

Barkanmu da sake saduwa daku a wannan fili namu, a wannan makon zamu so jin ra’ayoyinku a kan sabon yajin aikin da Kungiyar Malaman Jami’o’i, ASUU ta kara shiga bayan shafe wata 6 ana ja-in-ja tsakaninta ga Gwamnatin Tarayya. Menene ra’ayinku a kan albashin wata shida da ASUU ta bukaci a biya mambobinta? Wane mataki yakamata Gwamnatin ta dauka?

Adamu Yunusa Ibrahim

Maganar gaskiya wannan yajin aiki da Kungiyar Malamai ta ASUU ke yi kaifin Gwamnatin Tarayya ne. Kasancewar babu ‘ya’yansu a Jami’o’in gida Nijeriya ne ya sa Sam harkar ilimin ba ta gabansu. Kamar yadda suka kashe makarantun Primary da Secondary, har ta kawo sai wadanda ba su da yadda za su yi ne su ke tura yaransu makarantun. Saboda babu kwararrun malamai babu kayan aiki babu azuzuwan da yara ke zama don daukar darasi, idan ma akwai ajin babu kujeru. Hakan ya sa duk mai son yarona ya yi karatu sai dai ya kai shi makarantar kudi. Haka su ke so su ma Jami’o’in Nijeriya su koma. Domin yajin aikin da ASUU ke yi, ba a kan inganta albashin malamai kawai ake yi ba. Akwai alkawuran da Gwamnati ta dauka wajen samar da kudin yin gine-ginen azuzuwa da daliban kwanan dalibai da dakunan Gwaje-gwaje da dakunan Karatu na zamani mai dauke da na’urorin zamani da yara za su yi bincike domin inganta karatunsu. Duk wadannan na daga cikin abubuwan da Gwamnati ta kasa yi a Jami’o’in gida Nijeriya. Wata matsalar kuma ita ce yadda su ke son yin mummunan karin kudin makaranta da zai gagari Dan me karas da Dan me Yalo, biyan kudin makarantar. Hakan ya sa ba tare da la’akarin komai ba, su ke ta bayar da lasisin bude sabbin Jami’o’i masu zaman Kansu. Da yadda dan Talakan kasa zai gagara yin karatun sai yaransu. Tunda su ne ke tsabar kudi a ajiye da kadarorin da wasu ma ba su san iyakar su ba. Batun biyan Albashin Malamai na wata shida da wasu wata shidan da za su zo nan gaba, wannan ko tantama babu wajibi ne a biya. Domin shi aikin koyarwa a Jami’a ba kamar aikin gidan Burodi ba ne. Aiki ne da ya tattaro mutane masu ilimi da fikira da kuma hangen nesa. Kamar yadda shugaban ASUU na kasa Farfesa Emanuel Osodoke ya bayyana cewa, “Ko gobe Gwamnati Na iya kawo Karshen yajin aikin idan tana so”. Allah ya taimaki kasarmu Nijeriya da Jami’o’in gida Nijeriya. Amin.

ADVERTISEMENT

Kwamrade Adamu Yunusa Ibrahim, Malami a Cibiyar Nazarin Hausa, Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sakkwato, Nijeriya.

Mahdee Bashir

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

To nikam tunda a Nijeriya muke kuma mun san matsalolin kasarmu, wanda hatta tsaro ko harkar lafiya bai dameta ba balle ilimi, Dubi ga wagga batu innine ASUU dancen kafewa bai taso ba, tunda sunsan ba lalle a biya musu bukatunsu ba, saboda haka ko don daliba sai su yi hakuri a lallaba har Allah yakawo mana mafita, wannan raayi nane

Yusuf Muhammad Jalingo

Ra’ayina a nan, shi ne lallai laifin gwamnati ne saboda kowa a karkashinta yake, kuma dimokradiyya ce ta kawo gwamnatin kuma kowa na da ‘yancin ya nemi hakkinsa ta hanyar da ta dace kamar yadda ASUU ta yi sai dai gwamnati ta ba mu kunya don ba ta yi abin da ya dace ba . ASUU ta nemi abubuwa har bakwai amma gwamnati bata tabuka komai ba saboda tana nuna ko inkula a kan wannan lamari.

Sani Ladan

To a gaskiya tun da farko ita gwamnati ta yi sakaci har abin ya kazance haka kuma wannan shike nuni da cewa mafi yawan ‘yansiyasarmu basa mutunta harkar ilimin cikin gida sun fi kaunar su tura ‘ya’yansu makarantun Turai, ‘amma duk da haka suma ASUU ya kamata su duba ‘ya’yan talakawa su sassauta bukatunsu don samun mafita domin wadannan shugabannin basu da imani ko na kwabo daya kuma ba damuwarsu ba ne idan makarantu za su kai sheka 3 ba a bude ba ,amma komai suke yi Allah yana ganinsu kuma yana jiransu za su tarad dashi.

Baban Khairat

Kamata ya yi Malam nan su yi hakuri su duba yanayi da dalibai suke ciki na zaman gida ga lokaci na tafiya su janye saboda kishin kasa tunda su gwamnati an rasa samu daidaito ta wajensu. Allah ya kyauta

Kamal Y. Iyantama

Da ASUU din da Gwamnati duk wasa da hankalin talakawa suke yi, dukkansu muradun kansu suke karewa. Talaka ka ci gaba da kai wa Allah kuka.

Abdurrashid Ahmad Abubakar

Wannan lamari ya zama Inna lillahi wa Inna ilaihirraji’un, Allah ya kawo mana mafita kawai amma dukansu ba sa yi domin talaka.

Umar Ibrahim Umar

Ya zama wajibi gwamnati ta biya malamai hakkinsu saboda da ace ‘yan majalisa ne suke ya yin yajin aiki kana ganin gwamnati za ta hana su albashi ne, dan wannan wani sabon rikici ne da gwamnati ta dauko wanda zai kawo tsaiko mai tsawo da zai hana ‘ya’yan talakawan da suka zabi gwamnati karatu a kasarsu

Nazifi Haruna Iliyasu

Ni dai a nawa ra’ayin kamata ya yi gwamnati ta biya albashin su na wata 6 kana a zauna kuma ayi sulhu domin kyautata wa ‘ya’yan talakawa suma su sami ilimi, tunda ita gwamnati tana ikirari cewa ita ai ta talakawa ne.

Salihu Adamu

ASUU masu taurin kai. Da tun 2009 sun tsaya da an wuce wajen.

Ibraheem Yunuz

Mu dai don Allah a taimaka a janye ko mun koma makaranta don cigaba da karatu,wallahi mun gaji.

It’z Sam Dambatta

Babu abinda za mu ce da Allah sai godiya amma indai har gwamnati domin talakawa take yi to yakamata ace an magance matsalar nan tuntuni da ba wannan batun akeyi ba.

Shamsi Umar Bakanike Dambatta

Toh mudai sai dai muce Allah ya kawo karshen wannan yajin aiki da wannan kungiya ta ASUU suke yi.

ASUU
Aisha Seyoji
+ postsBio
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Ra’ayoyinku A Kan Ba Da Bashi Ga Daliban Manyan Makarantu
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Next Post
NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo

NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.