• Leadership Hausa
Wednesday, September 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku Kan Sabon Yajin Aiki Da ASUU Ta Tsunduma

by Aisha Seyoji
1 year ago
in Rahotonni
0
Ra’ayoyinku Kan Sabon Yajin Aiki Da ASUU Ta Tsunduma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Barkanmu da sake saduwa daku a wannan fili namu, a wannan makon zamu so jin ra’ayoyinku a kan sabon yajin aikin da Kungiyar Malaman Jami’o’i, ASUU ta kara shiga bayan shafe wata 6 ana ja-in-ja tsakaninta ga Gwamnatin Tarayya. Menene ra’ayinku a kan albashin wata shida da ASUU ta bukaci a biya mambobinta? Wane mataki yakamata Gwamnatin ta dauka?

Adamu Yunusa Ibrahim

Maganar gaskiya wannan yajin aiki da Kungiyar Malamai ta ASUU ke yi kaifin Gwamnatin Tarayya ne. Kasancewar babu ‘ya’yansu a Jami’o’in gida Nijeriya ne ya sa Sam harkar ilimin ba ta gabansu. Kamar yadda suka kashe makarantun Primary da Secondary, har ta kawo sai wadanda ba su da yadda za su yi ne su ke tura yaransu makarantun. Saboda babu kwararrun malamai babu kayan aiki babu azuzuwan da yara ke zama don daukar darasi, idan ma akwai ajin babu kujeru. Hakan ya sa duk mai son yarona ya yi karatu sai dai ya kai shi makarantar kudi. Haka su ke so su ma Jami’o’in Nijeriya su koma. Domin yajin aikin da ASUU ke yi, ba a kan inganta albashin malamai kawai ake yi ba. Akwai alkawuran da Gwamnati ta dauka wajen samar da kudin yin gine-ginen azuzuwa da daliban kwanan dalibai da dakunan Gwaje-gwaje da dakunan Karatu na zamani mai dauke da na’urorin zamani da yara za su yi bincike domin inganta karatunsu. Duk wadannan na daga cikin abubuwan da Gwamnati ta kasa yi a Jami’o’in gida Nijeriya. Wata matsalar kuma ita ce yadda su ke son yin mummunan karin kudin makaranta da zai gagari Dan me karas da Dan me Yalo, biyan kudin makarantar. Hakan ya sa ba tare da la’akarin komai ba, su ke ta bayar da lasisin bude sabbin Jami’o’i masu zaman Kansu. Da yadda dan Talakan kasa zai gagara yin karatun sai yaransu. Tunda su ne ke tsabar kudi a ajiye da kadarorin da wasu ma ba su san iyakar su ba. Batun biyan Albashin Malamai na wata shida da wasu wata shidan da za su zo nan gaba, wannan ko tantama babu wajibi ne a biya. Domin shi aikin koyarwa a Jami’a ba kamar aikin gidan Burodi ba ne. Aiki ne da ya tattaro mutane masu ilimi da fikira da kuma hangen nesa. Kamar yadda shugaban ASUU na kasa Farfesa Emanuel Osodoke ya bayyana cewa, “Ko gobe Gwamnati Na iya kawo Karshen yajin aikin idan tana so”. Allah ya taimaki kasarmu Nijeriya da Jami’o’in gida Nijeriya. Amin.

Kwamrade Adamu Yunusa Ibrahim, Malami a Cibiyar Nazarin Hausa, Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sakkwato, Nijeriya.

Mahdee Bashir

Labarai Masu Nasaba

Manyan Hafsoshin Sojin Nijeriya Da Suka Fafata Yakin Biyafara

Zargin Daura Aure Da Mai Kanjamau: Yadda Aka Tube Hakimi A Katsina

To nikam tunda a Nijeriya muke kuma mun san matsalolin kasarmu, wanda hatta tsaro ko harkar lafiya bai dameta ba balle ilimi, Dubi ga wagga batu innine ASUU dancen kafewa bai taso ba, tunda sunsan ba lalle a biya musu bukatunsu ba, saboda haka ko don daliba sai su yi hakuri a lallaba har Allah yakawo mana mafita, wannan raayi nane

Yusuf Muhammad Jalingo

Ra’ayina a nan, shi ne lallai laifin gwamnati ne saboda kowa a karkashinta yake, kuma dimokradiyya ce ta kawo gwamnatin kuma kowa na da ‘yancin ya nemi hakkinsa ta hanyar da ta dace kamar yadda ASUU ta yi sai dai gwamnati ta ba mu kunya don ba ta yi abin da ya dace ba . ASUU ta nemi abubuwa har bakwai amma gwamnati bata tabuka komai ba saboda tana nuna ko inkula a kan wannan lamari.

Sani Ladan

To a gaskiya tun da farko ita gwamnati ta yi sakaci har abin ya kazance haka kuma wannan shike nuni da cewa mafi yawan ‘yansiyasarmu basa mutunta harkar ilimin cikin gida sun fi kaunar su tura ‘ya’yansu makarantun Turai, ‘amma duk da haka suma ASUU ya kamata su duba ‘ya’yan talakawa su sassauta bukatunsu don samun mafita domin wadannan shugabannin basu da imani ko na kwabo daya kuma ba damuwarsu ba ne idan makarantu za su kai sheka 3 ba a bude ba ,amma komai suke yi Allah yana ganinsu kuma yana jiransu za su tarad dashi.

Baban Khairat

Kamata ya yi Malam nan su yi hakuri su duba yanayi da dalibai suke ciki na zaman gida ga lokaci na tafiya su janye saboda kishin kasa tunda su gwamnati an rasa samu daidaito ta wajensu. Allah ya kyauta

Kamal Y. Iyantama

Da ASUU din da Gwamnati duk wasa da hankalin talakawa suke yi, dukkansu muradun kansu suke karewa. Talaka ka ci gaba da kai wa Allah kuka.

Abdurrashid Ahmad Abubakar

Wannan lamari ya zama Inna lillahi wa Inna ilaihirraji’un, Allah ya kawo mana mafita kawai amma dukansu ba sa yi domin talaka.

Umar Ibrahim Umar

Ya zama wajibi gwamnati ta biya malamai hakkinsu saboda da ace ‘yan majalisa ne suke ya yin yajin aiki kana ganin gwamnati za ta hana su albashi ne, dan wannan wani sabon rikici ne da gwamnati ta dauko wanda zai kawo tsaiko mai tsawo da zai hana ‘ya’yan talakawan da suka zabi gwamnati karatu a kasarsu

Nazifi Haruna Iliyasu

Ni dai a nawa ra’ayin kamata ya yi gwamnati ta biya albashin su na wata 6 kana a zauna kuma ayi sulhu domin kyautata wa ‘ya’yan talakawa suma su sami ilimi, tunda ita gwamnati tana ikirari cewa ita ai ta talakawa ne.

Salihu Adamu

ASUU masu taurin kai. Da tun 2009 sun tsaya da an wuce wajen.

Ibraheem Yunuz

Mu dai don Allah a taimaka a janye ko mun koma makaranta don cigaba da karatu,wallahi mun gaji.

It’z Sam Dambatta

Babu abinda za mu ce da Allah sai godiya amma indai har gwamnati domin talakawa take yi to yakamata ace an magance matsalar nan tuntuni da ba wannan batun akeyi ba.

Shamsi Umar Bakanike Dambatta

Toh mudai sai dai muce Allah ya kawo karshen wannan yajin aiki da wannan kungiya ta ASUU suke yi.

Tags: ASUUHirara'ayoyiYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane 9 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata A Wani Hatsarin Mota Da Ya Rutsa Da Su A Abuja

Next Post

NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo

Related

Biyafara
Rahotonni

Manyan Hafsoshin Sojin Nijeriya Da Suka Fafata Yakin Biyafara

3 days ago
Kanjamau
Rahotonni

Zargin Daura Aure Da Mai Kanjamau: Yadda Aka Tube Hakimi A Katsina

3 days ago
Arewa maso Gabas
Rahotonni

A Dau Darasi Daga Asarar Dala Biliyan 100 Sakamakon Rikicin Arewa Maso Gabas

5 days ago
Kotu Ta Yanke Wa Wani Tsoho Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Har Abada Kan Laifin Fyade A Jigawa
Rahotonni

Kotu Ta Daure Wata Matashiya Kan Satar Katin Waya Na ₦275,400 A Kaduna

1 week ago
Bukatar Kulawa Ta Musamman Ga Tarbiyar ‘Ya’ya Maza
Rahotonni

Bukatar Kulawa Ta Musamman Ga Tarbiyar ‘Ya’ya Maza

2 weeks ago
Cikar Gwamnoni Kwana 100 A Karagar Mulki: Me Aka Tabuka A Jigawa, Bauchi, Nasarawa, Gombe, Borno Da Yobe?
Rahotonni

Cikar Gwamnoni Kwana 100 A Karagar Mulki: Me Aka Tabuka A Jigawa, Bauchi, Nasarawa, Gombe, Borno Da Yobe?

3 weeks ago
Next Post
NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo

NIS Ta Sake Lashe Kambun Gwarzuwar Hukuma Mafi Kwazo

LABARAI MASU NASABA

Hatsaniya Ta Kaure Kan Zargin Cirewa Wata Gawa Ido Daya A Asibitin Kwararru Da Ke Gombe

Hatsaniya Ta Kaure Kan Zargin Cirewa Wata Gawa Ido Daya A Asibitin Kwararru Da Ke Gombe

September 26, 2023
NNPP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamnan Kano Da Ta Ba Gawuna Nasara

NNPP Ta Kai Korafinta Ga Hukumar NJC Kan Kalaman Daya Da Cikin Alkalan Kotun Zaben Kano

September 26, 2023
Duniya

Ra’ayin Gina Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ta Bai Daya Na Tattaro Karfin Sauya Duniya

September 26, 2023
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina

‘Yansandan Jihar Nasarawa Ta Tabbatar Da Sace Wasu Daliba A Jihar

September 26, 2023
JKS

Babban Jami’in JKS: Kasar Sin Za Ta Karfafa Hadin Gwiwa Da Amincewa Da Juna Da Kasar Masar

September 26, 2023
Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango

NLC Da TUC Sun Shirya Tsunduma Yajin Aiki Mai Dogon Zango Ranar Talata 3 Ga Oktoba 2023

September 26, 2023
Kasar Sin Mai Burin Ganin Ci Gaban Kowa

Kasar Sin Mai Burin Ganin Ci Gaban Kowa

September 26, 2023
Da Alamun SAKA Ba Zai Buga Wasa Biyu Ba Saboda Raunin Da Ya Samu Arteta

Da Alamun SAKA Ba Zai Buga Wasa Biyu Ba Saboda Raunin Da Ya Samu Arteta

September 26, 2023
Kimiyya

Masana Kimiyya Na Kasashen Kenya Da Sin Sun Kaddamar Da Kundin Farko Game Da Nau’ikan Tsirran Da Kenya Ta Wallafa

September 26, 2023
Libya

Me Ya Haifar Da Ambaliya A Libya?

September 26, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.