• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Lafiyar Ƙwaƙwalwa Ta Duniya: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Horas Da ‘Yan Jarida A Abuja

Akwai 'Yan Nijeriya Miliyan 20 Da Ke Fama Da Matsalar Ƙwakwalwa

by yahuzajere
2 years ago
Dandazon 'yan jaridar da aka horas tare da kwararrun da suka bayar da horo bayan kammala horaswar a ranar Talata

Dandazon 'yan jaridar da aka horas tare da kwararrun da suka bayar da horo bayan kammala horaswar a ranar Talata

Majalisar Ɗinkin Duniya ta shirya horaswa ta musamman ga ‘yan jarida daga ɓangarori daban-daban a kan muhimmancin kula da lafiyar ƙwaƙwalwa domin taimaka wa wayar da kan jama’a game da abubuwan da ke shafar lafiyar ƙwaƙwalwa da yadda za a magance su ko a rage kaifinsu.

A yayin horaswar masana daban-daban sun gabatar da ƙasidu da suka yi bayani game da ‘yancin Ɗan’adam wajen samun kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa da muhimmancin abin da matakan riga-kafin kamuwa da cututtukan da suka shafi ƙwaƙwalwa.

  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada ‘Yancin Dan Adam Wajen Samun Kiwon Lafiyar Kwakwalwa
  • Kisan Dan Jarida: ‘Yansandan Sun Kama Wadanda ake Zargi Da Hannu A Zamfara

Bugu da ƙari an horas da ‘yan jaridan a kan alaƙar aikinsu da kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa da yadda ya kamata su riƙa bayar da rahotannin da suka shafi kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa cikin ƙwarewa da tausayawa.

Wakazalika, an aiwatar da wasu tsare-tsare na gwajin lafiyar ƙwaƙwalwar mahalartan domin kowa ya san matsayinsa da irin matakan da suka kamata mutum ya ɗauka domin daidaita rayuwarsa ta yadda ba za ta haifar masa da matsalar ƙwaƙwalwa ba.

ƙwaƙwalwa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

An fara gabatar da bikin ranar kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa ne a ranar 10 ga watan Oktobar 1992 ta hannun Ƙungiyar Kula da Lafiyar Ƙwaƙwalwa ta Duniya bisa goyon bayan Hukumar Lafiya ta Duniya da sauransu.

A saƙonsa na bikin ranar ta bana, Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres ya bayyana cewa, lafiyar ƙwaƙwalwa da tunani mai kyau yana ba Ɗan’adam damar gudanar da rayuwa mai gamsarwa da ba da gudummawa sosai ga al’ummomi.

Ya nuna takaicinta cewa, daya cikin mutane takwas a duniya na fama da matsalar lafiyar ƙwaƙwalwa, wanda hakan ya fi ƙamari cikin ‘yan mata da matasa.

ƙwaƙwalwa

Bugu da ƙari, mutum uku cikin mutane huɗu da ke fama da matsalar ƙwaƙwalwa, ba su samun isasshiyar kulawa ko kuma babu kulawa ma kwata-kwata, sannan da yawa suna fuskantar ƙyama da wariya a cikin al’umma.

“Kiyaye Lafiyar ƙwaƙwalwa ba gata ba ce ta wane da wane, haƙƙi ce ta dukkan Ɗan’adam– ya zama dole a kula da Lafiyar ƙwaƙwalwa a duk cikin al’ummatai da ke cikin faɗin duniyarmu. Dole ne gwamnatoci su ba da kulawa don magani ga masu matsalar ƙwaƙwalwa da kuma kiyaye hakkinsu.

“Dole ne kuma a magance matsalar cin zarafi tare da karya duk wani shingen da ke hana mutane neman tallafi don magance matsalar ƙwaƙwalwa kuma dole ne mu magance matsalar ƙwaƙwalwa tun daga tushe musamman ta fuskar talauci, wariya, tashin hankali da sauransu.

“A wannan rana ta kula da Kiwon Lafiyar Hankali ta Duniya, muna sake jaddada cewa, kiyaye lafiyar ƙwaƙwalwa, hakki ce kuma ‘yancin Ɗan’adam ne ba tare da nuna wata wariya ba, tare za mu gina duniya mafi ƙoshin lafiya inda kowa zai yi alfahari da ita” in ji ji sakataren majalisar.

ƙwaƙwalwa

Wata ƙididdiga da wata ƙwararriyar da ta yi lacca a taron horas da ‘yan jaridar, Mrs. Moji Makanjuola ta bayyana, ta nunar da cewa akwai ‘Yan Nijeriya aƙalla miliyan 20 da ke fama da rashin lafiyar ƙwaƙwalwa, sannan du-du-du asibitocin da ke kula da masu matsalar ƙwaƙwalwa na gwamnati ba su wuce guda takwas ba, da na masu zaman kansu guda 30, kana likitocin ƙwaƙwalwa 350 ne kacal ake da su a duk faɗin Nijeriya.

 

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Next Post
Alkalan Wasan Firimiya Sun Dauki Matakan Guje Wa Kuskure Dangane Da Na’urar VAR

Alkalan Wasan Firimiya Sun Dauki Matakan Guje Wa Kuskure Dangane Da Na'urar VAR

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.