• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Yaki Da Shaye Shaye Ta Duniya: Dr. Fauziyya Ta Tunatar Da Iyaye Aikin Dake Gabansu

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
Fauziyya

Ranar 26 ga wata June ne Majalisar Dunkin duniya ta ware domin yin Nazarin Kan Matsalar shaye shayen miyagun Kwayoyi a tsakanin al’umma.

mashawarciya ta musamman Kan Harkokin Lafiya ga Gwamna Ganduje, Shugabar Kwamitin Yaki da shaye-shaye ta Jihar Kano sannan kuma Shugabar Kwamitin Lura da masu cutar kwakwalwa Dr. Fauziyya Buba Idris ce ta bayyana Haka alokacin taron Manema labarai data gudanar a ofishinta.

  • Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

“Sanin kowa ne yadda Annobar Korana ta haifarwa da Duniya mummunar matsàla da har yanzu kokarin farfadowa ake daga illar da annobar ta yiwa duniya. Wannan ne babban dalilin da yasa dole a yiwa Matsalar shaye shayen Miyagun Kwayoyi kallon tsanaki tare da hada hannu da dukkan masu ruwa da tsaki domin fatattakar wannan matsala da ahalin ke neman zamewa al’umma babban kalubalen.

Dr. Fauziyya Buba Idris ta ci gaba da bayyana cewa wannan Rana Ce da Majalisar duniya ta ware domin yin Nazarin tare da bincika yadda za’a dakile wannan annoba ta shaye shayen Miyagun Kwayoyi da yanzu ke neman Zama wata gagarumar matsàla tsakanin matasa maza da matan wannan lokaci. Tace lamarin na tayarwa da duk wani Mai kishin cigaban al’umma hankali.

Hakazalika Kwararriyar masaniyar matsalolin Mata (Gani) ta bayyana cewa duk matsalolin Da ahalin yanzu Suka addabi Jama’a Ba su Wuce wannan Matsalar ta shaye shaye ba, “Idan aka tsinci Kai a irin wannan matsala daga ita ne ake fadawa sace sace, Matsalar Daba, fashi da makami, Garkuwan da Mutane fyade da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Tace domin Kawo karshen wannan matsala a Jihar Kano, Gwamna Dakta Abdullahu Umar Ganduje ya kafa wani kwakkwaran Kwamitin Mai mutanen 11 wadanda suke aiki ba dare ba Rana Wajen zakulo hanyoyin dakile yaduwar wannan mummunar ta’ada. Zuwa yanzu alhamdulillahi ana samu gagarumin ci gaba a aikin da ake na magance wannan matsala.

Taken taron na bana shi ne “Ya Za’ayi a samu hanyar Warware wannan matsala Baki Daya” yin hakan Kuma aiki ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa da ake Bukatar Hana hannu domin dakile wannan annoba. Don Haka sai ta shawarci iyaye dasu Kara kaimi Wajen Lura da wadanda yaransu ke mu’amala dasu domin gudun kitso da kwarkwata.

Saboda kyakkyawan fatan da ake dashi, Gwamnatin Jihar Kano ta kafa Kwamitocin tun daga matakin Kananan Hukumomin har zuwa mazabu, wanda kowa ne magidanci zai iya zuwa domin samun Karin haske akan wannan lamari tare da sanar da hukumomi irin halin da wasu yaran ke ciki.

A karshe Dr. Fauziyya ta jinjinawa kokarin da Gwamnati keyi na dakile wannan annoba, sannan ta godewa iyayen Kasa bisa hadin Kan suke bayarwa aduk lokacin da Bukatar Haka ta taso, musamman batun fadakarwa da Wayar da Kan Jama’a Baki Daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
Dalilan Da Ya Sa Muka Halatta Sayen Bindiga Don Kare Kai —Gwamnatin Zamfara

Dalilan Da Ya Sa Muka Halatta Sayen Bindiga Don Kare Kai —Gwamnatin Zamfara

LABARAI MASU NASABA

TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.