• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Yaki Da Shaye Shaye Ta Duniya: Dr. Fauziyya Ta Tunatar Da Iyaye Aikin Dake Gabansu

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Rahotonni
0
Ranar Yaki Da Shaye Shaye Ta Duniya: Dr. Fauziyya Ta Tunatar Da Iyaye Aikin Dake Gabansu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 26 ga wata June ne Majalisar Dunkin duniya ta ware domin yin Nazarin Kan Matsalar shaye shayen miyagun Kwayoyi a tsakanin al’umma.

mashawarciya ta musamman Kan Harkokin Lafiya ga Gwamna Ganduje, Shugabar Kwamitin Yaki da shaye-shaye ta Jihar Kano sannan kuma Shugabar Kwamitin Lura da masu cutar kwakwalwa Dr. Fauziyya Buba Idris ce ta bayyana Haka alokacin taron Manema labarai data gudanar a ofishinta.

  • Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

“Sanin kowa ne yadda Annobar Korana ta haifarwa da Duniya mummunar matsàla da har yanzu kokarin farfadowa ake daga illar da annobar ta yiwa duniya. Wannan ne babban dalilin da yasa dole a yiwa Matsalar shaye shayen Miyagun Kwayoyi kallon tsanaki tare da hada hannu da dukkan masu ruwa da tsaki domin fatattakar wannan matsala da ahalin ke neman zamewa al’umma babban kalubalen.

Dr. Fauziyya Buba Idris ta ci gaba da bayyana cewa wannan Rana Ce da Majalisar duniya ta ware domin yin Nazarin tare da bincika yadda za’a dakile wannan annoba ta shaye shayen Miyagun Kwayoyi da yanzu ke neman Zama wata gagarumar matsàla tsakanin matasa maza da matan wannan lokaci. Tace lamarin na tayarwa da duk wani Mai kishin cigaban al’umma hankali.

Hakazalika Kwararriyar masaniyar matsalolin Mata (Gani) ta bayyana cewa duk matsalolin Da ahalin yanzu Suka addabi Jama’a Ba su Wuce wannan Matsalar ta shaye shaye ba, “Idan aka tsinci Kai a irin wannan matsala daga ita ne ake fadawa sace sace, Matsalar Daba, fashi da makami, Garkuwan da Mutane fyade da sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Tace domin Kawo karshen wannan matsala a Jihar Kano, Gwamna Dakta Abdullahu Umar Ganduje ya kafa wani kwakkwaran Kwamitin Mai mutanen 11 wadanda suke aiki ba dare ba Rana Wajen zakulo hanyoyin dakile yaduwar wannan mummunar ta’ada. Zuwa yanzu alhamdulillahi ana samu gagarumin ci gaba a aikin da ake na magance wannan matsala.

Taken taron na bana shi ne “Ya Za’ayi a samu hanyar Warware wannan matsala Baki Daya” yin hakan Kuma aiki ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa da ake Bukatar Hana hannu domin dakile wannan annoba. Don Haka sai ta shawarci iyaye dasu Kara kaimi Wajen Lura da wadanda yaransu ke mu’amala dasu domin gudun kitso da kwarkwata.

Saboda kyakkyawan fatan da ake dashi, Gwamnatin Jihar Kano ta kafa Kwamitocin tun daga matakin Kananan Hukumomin har zuwa mazabu, wanda kowa ne magidanci zai iya zuwa domin samun Karin haske akan wannan lamari tare da sanar da hukumomi irin halin da wasu yaran ke ciki.

A karshe Dr. Fauziyya ta jinjinawa kokarin da Gwamnati keyi na dakile wannan annoba, sannan ta godewa iyayen Kasa bisa hadin Kan suke bayarwa aduk lokacin da Bukatar Haka ta taso, musamman batun fadakarwa da Wayar da Kan Jama’a Baki Daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hajjin Bana: Gwamna Bagudu Ya Nada Ministan Shari’a Amirul-Hajj Na Jihar Kebbi

Next Post

Dalilan Da Ya Sa Muka Halatta Sayen Bindiga Don Kare Kai —Gwamnatin Zamfara

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

5 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 week ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

1 week ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

3 weeks ago
Next Post
Dalilan Da Ya Sa Muka Halatta Sayen Bindiga Don Kare Kai —Gwamnatin Zamfara

Dalilan Da Ya Sa Muka Halatta Sayen Bindiga Don Kare Kai —Gwamnatin Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.