ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Yaki Da Shaye Shaye Ta Duniya: Dr. Fauziyya Ta Tunatar Da Iyaye Aikin Dake Gabansu

by Abdullahi Muh'd Sheka
4 years ago
Fauziyya

Ranar 26 ga wata June ne Majalisar Dunkin duniya ta ware domin yin Nazarin Kan Matsalar shaye shayen miyagun Kwayoyi a tsakanin al’umma.

mashawarciya ta musamman Kan Harkokin Lafiya ga Gwamna Ganduje, Shugabar Kwamitin Yaki da shaye-shaye ta Jihar Kano sannan kuma Shugabar Kwamitin Lura da masu cutar kwakwalwa Dr. Fauziyya Buba Idris ce ta bayyana Haka alokacin taron Manema labarai data gudanar a ofishinta.

  • Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

“Sanin kowa ne yadda Annobar Korana ta haifarwa da Duniya mummunar matsàla da har yanzu kokarin farfadowa ake daga illar da annobar ta yiwa duniya. Wannan ne babban dalilin da yasa dole a yiwa Matsalar shaye shayen Miyagun Kwayoyi kallon tsanaki tare da hada hannu da dukkan masu ruwa da tsaki domin fatattakar wannan matsala da ahalin ke neman zamewa al’umma babban kalubalen.

ADVERTISEMENT

Dr. Fauziyya Buba Idris ta ci gaba da bayyana cewa wannan Rana Ce da Majalisar duniya ta ware domin yin Nazarin tare da bincika yadda za’a dakile wannan annoba ta shaye shayen Miyagun Kwayoyi da yanzu ke neman Zama wata gagarumar matsàla tsakanin matasa maza da matan wannan lokaci. Tace lamarin na tayarwa da duk wani Mai kishin cigaban al’umma hankali.

Hakazalika Kwararriyar masaniyar matsalolin Mata (Gani) ta bayyana cewa duk matsalolin Da ahalin yanzu Suka addabi Jama’a Ba su Wuce wannan Matsalar ta shaye shaye ba, “Idan aka tsinci Kai a irin wannan matsala daga ita ne ake fadawa sace sace, Matsalar Daba, fashi da makami, Garkuwan da Mutane fyade da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Tace domin Kawo karshen wannan matsala a Jihar Kano, Gwamna Dakta Abdullahu Umar Ganduje ya kafa wani kwakkwaran Kwamitin Mai mutanen 11 wadanda suke aiki ba dare ba Rana Wajen zakulo hanyoyin dakile yaduwar wannan mummunar ta’ada. Zuwa yanzu alhamdulillahi ana samu gagarumin ci gaba a aikin da ake na magance wannan matsala.

Taken taron na bana shi ne “Ya Za’ayi a samu hanyar Warware wannan matsala Baki Daya” yin hakan Kuma aiki ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa da ake Bukatar Hana hannu domin dakile wannan annoba. Don Haka sai ta shawarci iyaye dasu Kara kaimi Wajen Lura da wadanda yaransu ke mu’amala dasu domin gudun kitso da kwarkwata.

Saboda kyakkyawan fatan da ake dashi, Gwamnatin Jihar Kano ta kafa Kwamitocin tun daga matakin Kananan Hukumomin har zuwa mazabu, wanda kowa ne magidanci zai iya zuwa domin samun Karin haske akan wannan lamari tare da sanar da hukumomi irin halin da wasu yaran ke ciki.

A karshe Dr. Fauziyya ta jinjinawa kokarin da Gwamnati keyi na dakile wannan annoba, sannan ta godewa iyayen Kasa bisa hadin Kan suke bayarwa aduk lokacin da Bukatar Haka ta taso, musamman batun fadakarwa da Wayar da Kan Jama’a Baki Daya.

Fauziyya
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
Rahotonni

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Next Post
Dalilan Da Ya Sa Muka Halatta Sayen Bindiga Don Kare Kai —Gwamnatin Zamfara

Dalilan Da Ya Sa Muka Halatta Sayen Bindiga Don Kare Kai —Gwamnatin Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.