• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

by Yusuf Shuaibu
3 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rashin ganin shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Kano a ziyarar ta’aziyya da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya kai ga iyalin Marigayin Alhaji Aminu Dantata, ya haifar da zazzafar muhawara a cikin jam’iyyar.

Rahotanni sun bayyana cewa yayin da jami’an gwamnatin Jihar Kano da ke cikin jam’iyyar NNPP suka yi tururuwan tarbar mataimakin shugaban kasan, ba a ga duriyar shugabannin jam’iyyar APC na jihar ba a wurin wannan taron da ya gudana a ranar Alhamis.

  • Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
  • Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

Wannan lamari ya haifar da alamomin tambaya, yayin da wasu suna zargin cewa akwai rashi jituwa a cikin APC bayan saukar Dakta Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa.

Ganduje ya kasance tsohon gwamnan Jihar Kano, wanda har yanzu ke da tasiri a cikin harkokin siyasar jihar, ya yi murabus daga mukamin shugaban APC a ranar 27 ga Yuni, sakamakon lissafin siyasa da shirye-shiryen da aka yi a cikin jam’iyyar kafin zaben 2027.

Masana harkokin siyasa suna ganin cewa wasu daga cikin shugabannin APC a jihar ba su yi farin ciki da murabus din Ganduje a matsayin shugaban APC na kasa ba, kuma suna ganin cewa Shettima ya taka rawa wajen tilasta wa Ganduje yin murabus.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Rahotanin sun bayyana cewa Shettima ya ziyarci Kano ne don yin ta’aziyyar rasuwar hamshakin dan kasuwa, Alhaji Aminu Dantata, wanda ya rasu kwanan nan, da kuma jajanta wa mutanen Kano kan wannan rashi.

Haka kuma rahotannin sun bayyana cewa a irin wadannan manyan taruka a Nijeriya, an saba ganin shugabannin jam’iyya da goyon baya su tarbi manyan jami’ai kamar mataimakin shugaban kasa, amma lamarin ya bambanta yayin ziyarar Shettima, wanda ya haifar da zazzafar muhawara.

Da yake musanta cewa akwai rikice-rikice na cikin gida a jam’iyyar, sakataren APC a Kano, Ibrahim Zakari Sarina, ya shaida cewa rashin halartar shugabannin jam’iyyar a ziyarar ta’aziyya da mataimakin shugaban kasa ya kawo Kano ya faru ne sakamakon rashin sadarwa.

“Mun san cewa ziyarar za ta kasance, amma sadarwa ta zo a makare. Kafin mu shirya, mun riga mun makara. Saboda gwamnatin ta riga ta shirya tun kafin mu isa wurin.

“A gaskiya wannan abu ba ya da alaka da kowanne irin lamari na siyasa. An sanar da mu a makare, har ita kanta gwamnatin jihar a makare aka sanar da ita. Daga baya mun aike da godyarmu ga mataimakin shugaban kasa bisa ziyara, kuma ya fahimci yanayin sosai,” in ji Sarina.

Duk da wannan bayani, an samu rarrabuwan kai a tsakanin ‘yan siyasa a jihar.

Wani jigo a APC a yankin Gwale, Abdullahi Kabiru, ya bayyana cewa ya ji takaicin rashin halartar shugabannin jam’iyyar. “Wannan shi ne mataimakin shugaban kasa na wannan kasa, kuma ba mu kasa shirya tarba a gare shi ba? Wannan ba karamin kuskure ba ne. Ko da an samu rashin kyakkyawan sadarwa, yana nuna cewa akwai rashin hadin kai,” in ji shi.

Ita kuwa wata mai kishin jam’iyya, Amina Sani daga Tarauni, ra’ayinta ya sha bamban. Ta ce, “Na gamsu da bayanin da jam’iyyar ta bayar. Abubuwa suna faruwa a siyasa, musamman lokacin da jadawalin ke canzawa. Amma ina fatan hakan ba zai zama sabani ba. Dole ne mu girmama shugabanninmu da ofisoshinsu ba tare da la’akari da kowanne bambancin siyasa ba.”

Da yake jawabi kan lamarnin, wani masana harkokin siyasa, Dakta Musa Auwal ya bayyana cewa dole ne jam’iyyar ta yi taka-tsantsan. “Ko lamarin ya faru da gangan ko akasin haka, a duk lokacin da aka samu rarrabukan na manyan shugabannin jam’iyya a fili, yana rage karfin jam’iyyar kuma yana karfafa ‘yan adawa.

“APC a Kano tana taka muhimmiyar rawa a siyasan kasar nan, kuma kowanne takaddama da ke tasowa Kano na shugabancin ko na siyasa na iya zama babban lamari da ke daukan tsawon lokaci ana tattaunawa a kai,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCShettima
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Next Post

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Related

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

1 day ago
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

1 day ago
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

1 week ago
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

4 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

4 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

4 weeks ago
Next Post
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.