• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Buhari Ya Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Ya Same Ta, In Ji Adesina

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Rashin Tsaro: Buhari Ya Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Ya Same Ta, In Ji Adesina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi iyakacin kokarinsa wajen tunkarar kalubalen tsaro da Nijeriya ke fuskanta tun bayan hawansa mulki a watan Mayun 2015 “kuma yana barin kasar nan fiye da yadda ya same ta.”

Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels a Abuja.

  • Wang Wenbin: Ayyukan Masu Rajin Neman ’Yancin Kan Taiwan Barazana Ne Ga Tsaro
  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sanda Da Jikkata Wasu A Legas

A yayin da yake fuskantar kwararan bayanai da ke nuna cewa tsakanin watan Mayun 2015 zuwa Mayu 2022, sama da ‘yan Nijeriya 55,000 ne ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga da gungun ‘yan bindiga suka kashe, ya ce shugaban kasar nan ya bar yanayin tsaron kasar fiye da yadda ya same shi a shekarar 2015.

“Alkaluman yana raguwa a cikin shekaru da yawa kuma gaskiya ce ta kafa tarihi. Babu wanda zai iya canza shi,” in ji shi.

Da aka tambaye shi ko lamarin ya inganta, sai ya ce, “kwarai da gaske”.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

“A shekarar 2015 mun san inda Nijeriya ta ke. Akalla kananan hukumomi 17 na kasar nan suna karkashin ikon ‘yan tada kayar baya.

“Maganar kula, ina nufin suna zaune a fadar sarki, suna zaune a kujerun shugabannin kananan hukumomi. NYSC ba ta iya horar da masu yi wa kasa hidima a wasu yankuna.

“Yau wannan shi ne ke faruwa? A’a, sarakunan sun koma cikin gidajensu. Shuwagabannin kananan hukumomin sun koma ofisoshinsu. Ana buɗlde wa masu yi wa kasa hidima na NYSC a wadannan jahohin kuma ana tura ma’aikatan zuwa jihohin. Yanzu ana so a ce wannan ba sauyi ba ne? A’a, mu kasance masu gaskiya,” in ji kakakin shugaban.

Ya kuma ce nadin shugabannin ma’aikatun bai shafi daidaita kabilanci da ka’idar tarayya ba, inda ya ce shugaban kasa yana da hurumin zaben wadanda yake ganin za su iya tabbatar da kasar nan.

“Kada ku sanya tsaro ga daidaiton kabilanci, kada ku sanya tsaro ga halin tarayya. Hasali ma, kundin tsarin mulkin da ya bayyana halin tarayya har ma ya bai wa shugaban kasa wasu hukunce-hukuncen da zai iya yi da kansa,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariFemi AdesinaMulkiTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Birtaniya Ta Haramta Daukar Likitoci ‘Yan Nijeriya Aiki

Next Post

Gwamnatin Bauchi Ta Ja Kunnen Masu Wa’azi Kan Amfani Da Kalaman Tunzura Jama’a

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 day ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Gwamnatin Bauchi Ta Ja Kunnen Masu Wa’azi Kan Amfani Da Kalaman Tunzura Jama’a

Gwamnatin Bauchi Ta Ja Kunnen Masu Wa'azi Kan Amfani Da Kalaman Tunzura Jama'a

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Adesina

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.