• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Buhari Ya Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Ya Same Ta, In Ji Adesina

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Rashin Tsaro: Buhari Ya Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Ya Same Ta, In Ji Adesina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi iyakacin kokarinsa wajen tunkarar kalubalen tsaro da Nijeriya ke fuskanta tun bayan hawansa mulki a watan Mayun 2015 “kuma yana barin kasar nan fiye da yadda ya same ta.”

Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels a Abuja.

  • Wang Wenbin: Ayyukan Masu Rajin Neman ’Yancin Kan Taiwan Barazana Ne Ga Tsaro
  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sanda Da Jikkata Wasu A Legas

A yayin da yake fuskantar kwararan bayanai da ke nuna cewa tsakanin watan Mayun 2015 zuwa Mayu 2022, sama da ‘yan Nijeriya 55,000 ne ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga da gungun ‘yan bindiga suka kashe, ya ce shugaban kasar nan ya bar yanayin tsaron kasar fiye da yadda ya same shi a shekarar 2015.

“Alkaluman yana raguwa a cikin shekaru da yawa kuma gaskiya ce ta kafa tarihi. Babu wanda zai iya canza shi,” in ji shi.

Da aka tambaye shi ko lamarin ya inganta, sai ya ce, “kwarai da gaske”.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

“A shekarar 2015 mun san inda Nijeriya ta ke. Akalla kananan hukumomi 17 na kasar nan suna karkashin ikon ‘yan tada kayar baya.

“Maganar kula, ina nufin suna zaune a fadar sarki, suna zaune a kujerun shugabannin kananan hukumomi. NYSC ba ta iya horar da masu yi wa kasa hidima a wasu yankuna.

“Yau wannan shi ne ke faruwa? A’a, sarakunan sun koma cikin gidajensu. Shuwagabannin kananan hukumomin sun koma ofisoshinsu. Ana buɗlde wa masu yi wa kasa hidima na NYSC a wadannan jahohin kuma ana tura ma’aikatan zuwa jihohin. Yanzu ana so a ce wannan ba sauyi ba ne? A’a, mu kasance masu gaskiya,” in ji kakakin shugaban.

Ya kuma ce nadin shugabannin ma’aikatun bai shafi daidaita kabilanci da ka’idar tarayya ba, inda ya ce shugaban kasa yana da hurumin zaben wadanda yake ganin za su iya tabbatar da kasar nan.

“Kada ku sanya tsaro ga daidaiton kabilanci, kada ku sanya tsaro ga halin tarayya. Hasali ma, kundin tsarin mulkin da ya bayyana halin tarayya har ma ya bai wa shugaban kasa wasu hukunce-hukuncen da zai iya yi da kansa,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariFemi AdesinaMulkiTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Birtaniya Ta Haramta Daukar Likitoci ‘Yan Nijeriya Aiki

Next Post

Gwamnatin Bauchi Ta Ja Kunnen Masu Wa’azi Kan Amfani Da Kalaman Tunzura Jama’a

Related

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

4 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

15 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

18 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

20 hours ago
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

1 day ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

2 days ago
Next Post
Gwamnatin Bauchi Ta Ja Kunnen Masu Wa’azi Kan Amfani Da Kalaman Tunzura Jama’a

Gwamnatin Bauchi Ta Ja Kunnen Masu Wa'azi Kan Amfani Da Kalaman Tunzura Jama'a

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.