• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Buhari Ya Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Ya Same Ta, In Ji Adesina

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Rashin Tsaro: Buhari Ya Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Ya Same Ta, In Ji Adesina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi iyakacin kokarinsa wajen tunkarar kalubalen tsaro da Nijeriya ke fuskanta tun bayan hawansa mulki a watan Mayun 2015 “kuma yana barin kasar nan fiye da yadda ya same ta.”

Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels a Abuja.

  • Wang Wenbin: Ayyukan Masu Rajin Neman ’Yancin Kan Taiwan Barazana Ne Ga Tsaro
  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sanda Da Jikkata Wasu A Legas

A yayin da yake fuskantar kwararan bayanai da ke nuna cewa tsakanin watan Mayun 2015 zuwa Mayu 2022, sama da ‘yan Nijeriya 55,000 ne ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga da gungun ‘yan bindiga suka kashe, ya ce shugaban kasar nan ya bar yanayin tsaron kasar fiye da yadda ya same shi a shekarar 2015.

“Alkaluman yana raguwa a cikin shekaru da yawa kuma gaskiya ce ta kafa tarihi. Babu wanda zai iya canza shi,” in ji shi.

Da aka tambaye shi ko lamarin ya inganta, sai ya ce, “kwarai da gaske”.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

“A shekarar 2015 mun san inda Nijeriya ta ke. Akalla kananan hukumomi 17 na kasar nan suna karkashin ikon ‘yan tada kayar baya.

“Maganar kula, ina nufin suna zaune a fadar sarki, suna zaune a kujerun shugabannin kananan hukumomi. NYSC ba ta iya horar da masu yi wa kasa hidima a wasu yankuna.

“Yau wannan shi ne ke faruwa? A’a, sarakunan sun koma cikin gidajensu. Shuwagabannin kananan hukumomin sun koma ofisoshinsu. Ana buɗlde wa masu yi wa kasa hidima na NYSC a wadannan jahohin kuma ana tura ma’aikatan zuwa jihohin. Yanzu ana so a ce wannan ba sauyi ba ne? A’a, mu kasance masu gaskiya,” in ji kakakin shugaban.

Ya kuma ce nadin shugabannin ma’aikatun bai shafi daidaita kabilanci da ka’idar tarayya ba, inda ya ce shugaban kasa yana da hurumin zaben wadanda yake ganin za su iya tabbatar da kasar nan.

“Kada ku sanya tsaro ga daidaiton kabilanci, kada ku sanya tsaro ga halin tarayya. Hasali ma, kundin tsarin mulkin da ya bayyana halin tarayya har ma ya bai wa shugaban kasa wasu hukunce-hukuncen da zai iya yi da kansa,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariFemi AdesinaMulkiTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Birtaniya Ta Haramta Daukar Likitoci ‘Yan Nijeriya Aiki

Next Post

Gwamnatin Bauchi Ta Ja Kunnen Masu Wa’azi Kan Amfani Da Kalaman Tunzura Jama’a

Related

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

2 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

13 hours ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

19 hours ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

24 hours ago
Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

1 day ago
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

2 days ago
Next Post
Gwamnatin Bauchi Ta Ja Kunnen Masu Wa’azi Kan Amfani Da Kalaman Tunzura Jama’a

Gwamnatin Bauchi Ta Ja Kunnen Masu Wa'azi Kan Amfani Da Kalaman Tunzura Jama'a

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.