• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida

byMuhammad
3 months ago
inManyan Labarai
0
Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida

Tsohon shugaban ƙasa, Janaral Ibrahim Badamasi Babagana ya bayyana alhininsa bisa rasuwar abokinsa kuma tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu ranar Lahadi 13, ga Yulin 2025 a wani asibiti da ke birnin Landan.

Babangida ya ce: “Ina cike da alhini da juyayi na samun labarin rasuwar abokina, ɗan’uwana, abokin karatuna a makarantar soja, kuma abokin gwagwarmayar gina ƙasa, Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, GCFR.”

  • Sarkin Musulmi, Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari
  • Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

“Mun fara haduwa da shi a shekarar 1962 lokacin da muka shiga Kwalejin Horan Sojoji ta Nijeriya da ke Kaduna. Tun daga wancan lokaci, Muhammadu Buhari ya fara bambanta kansa da saura, saboda mutum ne mai ƙarfin zuciya da tsarin rayuwa, kuma ɗan kishin ƙasa mai ƙaunar ci gaban Nijeriya. Mun sha wahala tare, mun kuma yi faɗi-tashi tare. Ƙaunar ƙasa da ƙwarewa a aiki su ne suka haɗa mu wuri guda, ba kawai aikin soji ba.” In ji Babangida

Janar Babagida ya ci gaba da cewa: “A cikin aikinmu, ƙaddara ta sa kowannenmu ya shugabanci Nijeriya a lokuta daban-daban da yanayi daban. Amma a kowane lokaci, Buhari ya kasance mai kishin gaskiya da bin tsarin mulki da martabar shugabanci. Ya yi wa Nijeriya hidima da amana da jajircewa ko da kuwa a wasu lokutan wasu ba su fahimce inda ya dosa ba.”

“Bayan aikin soji, na san shi a matsayin mutum mai tsoron Allah, wanda yake da nutsuwa da riƙo da addininsa, kuma yana rayuwa da tawali’u da rayuwa akan manufa. Duk da cewa ba koyaushe ra’ayinmu yake zuwa ɗaya ba, kamar yadda yake a tsakanin ‘yan uwa, amma ban taɓa shakkar gaskiyarsa ko kishin ƙasarsa ba,”

Labarai Masu Nasaba

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

“Rasuwar Buhari ba kawai rasa tsohon shugaban ƙasa ba ne, ko shugaban da aka zaɓa sau biyu a mulkin dimokuraɗiyya ba. Rasa shi babban rashin mutum ne wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen haɗa tsohuwar Nijeriya da sabuwar jamhuriya. Ko a lokacin da ya yi ritaya, ya kasance abin koyi da nagarta da gaskiya ga mutane da dama.”

A ƙarshe tsohon shugaban ƙasar, ya yi addu’a ga marigayi Buhari tare da miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga matarsa Aisha da ‘ya’yansa, da jikokinsa da dukkan jama’ar Nijeriya da ya yi wa hidima. “Allah ya gafarta masa, ya karɓi ayyukansa na alheri, ya kuma sanya shi a Aljannatul Firdaus.” In ji Janar Ibrahim Badamasi Babangida, tsohon shugaban Nijeriya, a cikin wani sakon ta’aziyya da ya aike a ranar Lahadi 13, Yuli 2025.

Tags: BabangidaLandanNijeriyaRasuwaRasuwar Buhari
ShareTweetSendShare
Muhammad

Muhammad

Related

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 
Manyan Labarai

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

6 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

10 hours ago
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu
Manyan Labarai

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

18 hours ago
Next Post
Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025
Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

October 6, 2025
Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

October 6, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Tinubu

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

October 6, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

October 6, 2025
Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.