• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida

by Muhammad
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon shugaban ƙasa, Janaral Ibrahim Badamasi Babagana ya bayyana alhininsa bisa rasuwar abokinsa kuma tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu ranar Lahadi 13, ga Yulin 2025 a wani asibiti da ke birnin Landan.

Babangida ya ce: “Ina cike da alhini da juyayi na samun labarin rasuwar abokina, ɗan’uwana, abokin karatuna a makarantar soja, kuma abokin gwagwarmayar gina ƙasa, Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, GCFR.”

  • Sarkin Musulmi, Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari
  • Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

“Mun fara haduwa da shi a shekarar 1962 lokacin da muka shiga Kwalejin Horan Sojoji ta Nijeriya da ke Kaduna. Tun daga wancan lokaci, Muhammadu Buhari ya fara bambanta kansa da saura, saboda mutum ne mai ƙarfin zuciya da tsarin rayuwa, kuma ɗan kishin ƙasa mai ƙaunar ci gaban Nijeriya. Mun sha wahala tare, mun kuma yi faɗi-tashi tare. Ƙaunar ƙasa da ƙwarewa a aiki su ne suka haɗa mu wuri guda, ba kawai aikin soji ba.” In ji Babangida

Janar Babagida ya ci gaba da cewa: “A cikin aikinmu, ƙaddara ta sa kowannenmu ya shugabanci Nijeriya a lokuta daban-daban da yanayi daban. Amma a kowane lokaci, Buhari ya kasance mai kishin gaskiya da bin tsarin mulki da martabar shugabanci. Ya yi wa Nijeriya hidima da amana da jajircewa ko da kuwa a wasu lokutan wasu ba su fahimce inda ya dosa ba.”

“Bayan aikin soji, na san shi a matsayin mutum mai tsoron Allah, wanda yake da nutsuwa da riƙo da addininsa, kuma yana rayuwa da tawali’u da rayuwa akan manufa. Duk da cewa ba koyaushe ra’ayinmu yake zuwa ɗaya ba, kamar yadda yake a tsakanin ‘yan uwa, amma ban taɓa shakkar gaskiyarsa ko kishin ƙasarsa ba,”

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

“Rasuwar Buhari ba kawai rasa tsohon shugaban ƙasa ba ne, ko shugaban da aka zaɓa sau biyu a mulkin dimokuraɗiyya ba. Rasa shi babban rashin mutum ne wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen haɗa tsohuwar Nijeriya da sabuwar jamhuriya. Ko a lokacin da ya yi ritaya, ya kasance abin koyi da nagarta da gaskiya ga mutane da dama.”

A ƙarshe tsohon shugaban ƙasar, ya yi addu’a ga marigayi Buhari tare da miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga matarsa Aisha da ‘ya’yansa, da jikokinsa da dukkan jama’ar Nijeriya da ya yi wa hidima. “Allah ya gafarta masa, ya karɓi ayyukansa na alheri, ya kuma sanya shi a Aljannatul Firdaus.” In ji Janar Ibrahim Badamasi Babangida, tsohon shugaban Nijeriya, a cikin wani sakon ta’aziyya da ya aike a ranar Lahadi 13, Yuli 2025.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BabangidaLandanNijeriyaRasuwaRasuwar Buhari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Next Post

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

Related

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

32 minutes ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

2 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

4 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

18 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

21 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

1 day ago
Next Post
Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.