• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ruguza Tsohon Tsari Na Duniya Zai Haifar Da Ci Gaban Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Ruguza Tsohon Tsari Na Duniya Zai Haifar Da Ci Gaban Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashen Afirka sun dade suna kasancewa masu samar da danyun kayayyaki da ma’adinai, a bisa tsarin samar da kayayyaki na duniya. Sai dai lokaci ya yi da za a kawo sauye-sauye.

 

A kwanan nan, a birnin Beijing na kasar Sin, ana gudanar da bikin baje kolin tsarin samar da kayayyaki na duniya a kasar Sin, wato CISCE, a karo na biyu, wanda ya kasance wani muhimmin dandalin da kasar Sin ta kafa don karfafa hadin kan kasashe daban daban, ta fuskar tsare-tsaren masana’antu da na samar da kayayyaki. Kana bikin na da ma’anar musamman ga kasar Sin, da kasashen dake nahiyar Afirka.

  • Ɗansanda Ya Gamu Da Ajalinsa Bayan Fasa Tukunyar Miya A Adamawa
  • Xi Ya Bukaci A Aiwatar Da Kudurin Kwamitin Sulhun MDD Kan Batun Palastinu

Wani babban dalilin da ya sa kasar Sin kafa bikin CISCE, shi ne domin tinkarar matakan da kasar Amurka da kawayenta na yammacin duniya suka dauka, na kin dunkulewar tattalin arzikin duniya waje guda. Wadannan kasashe suna neman rage tasirin kasar Sin a tsare-tsaren masana’antu da na samar da kayayyaki na duniya, ta yadda su da kansu za su sake hawa kujerar jagorancin tattalin arzikin duniya.

 

Labarai Masu Nasaba

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Hakika kasashen Afirka sun fahimci nau’in matakan kasar Amurka da na kawayenta sosai, saboda matakai ne na mai da wani saniyar ware, wadanda suka yi kama da matakan da ‘yan mulki mallaka suka dauka a nahiyar Afirka, kamarsu nuna bambancin launin fata, da tilasta wa nahiyar Afirka kasancewa a matsayin mai samar da danyun kayayyaki, da zama babbar kasuwar da ake sayar da kayayyakin masana’antu. A ganin Amurka da kawayenta, ta hanyar hana sauran kasashe tasowa, za su iya kare fifikonsu har abada. Amma dai kamar yadda aka kawar da manufar bambancin launin fata, duk wata manufar da aka tsara, in dai ba ta da adalci, to, tabbas ne za a kawo karshenta a wata rana.

 

Ko da yake tun daga lokacin mulkin mallaka, an dade ana amfani da tsohon tsarin tattalin arziki wajen danne kasashen Afirka, amma yanzu an fara samun sauyawar yanayi. Bisa wani rahoton da taron ciniki da batun ci gaba na Majalisar Dinkin Duniya, wato UNCTAD a takaice, ya gabatar, an ce don neman tinkarar matakan kin dunkulewar tattalin arzikin duniya, wasu sabbin masana’antu, irinsu na hada motoci, da kayayyakin latironi, da makamashin ake iya sabuntawa, da magunguna, da kayayyakin aikin jinya, da dai sauransu, suna kokarin raba bangarori masu samar musu da kayayyaki a wurare daban-daban, don magance yiwuwar katsewar hanyar samun kayan da ake bukata. Wannan yanayi, a cewar UNCTAD, na samar da damammaki ga kasashen Afirka, don su taka rawar gani a tsare-tsaren samar da kayayyaki na duniya.

 

An ce, kasashen Afirka za su iya amfani da fifikonsu na samun dimbin al’umma, da ma’adinai masu muhimmanci, wajen zama kasashen dake samar da sassan kayayyakin da ake bukata a wasu sabbin sana’o’i. Sai dai kafin su iya cimma wannan buri, ya kamata kasashen Afirka su inganta kayayyakinsu na more rayuwa, da horar da ma’aikata, da neman jari da fasahohin da suke bukata. Kana a wadannan fannoni, kasar Sin ta dade tana hadin gwiwa da kasashen Afirka, cikin wani yanayi mai gamsarwa.

 

Hakika duk wani tsohon tsari, idan aka ga an kawo karshensa a wata rana, tabbas domin yana haifar da rashin jin dadi a zukatan mutanen duniya ne. A nan za mu iya ba da misalin tashar jiragen ruwa ta Chankay ta kasar Peru, wadda aka gina da dalar Amurka biliyan 3.5, a hadin gwiwar kasashen Peru da Sin, tare da burin inganta aikin jigilar kayayyaki cikin tekun Fasifik. Bayan da aka kaddamar da tashar a kwanan baya, shugabannin kasashen Latin Amurka da dama sun bayyana farin cikinsu da kakkyawan fatan da aka sanya a aikin. Amma a nata bangare, gwamnatin Trump mai jiran gado ta kasar Amurka ta yi gargadin cewa, za ta karbi harajin kwastam da ya kai kaso 60%, kan dukkan kayayyakin da aka kai su kasar Amurka da aka bi ta tashar Chancay da su. Dalilin da ya sa take son daukar matakin kawai shi ne, Amurka ta ce, nasarar da aka samu a tashar Chancay za ta iya karfafa gwiwar sauran kasashen dake Latin Amurka su karfafa zumuntar dake tsakaninsu da kasar Sin.

 

Ta wannan misali za mu iya ganin yadda kasar Sin take kokarin hadin gwiwa da sauran kasashe, da tabbatar da moriyar juna, yayin da kasar Amurka ke neman saka takunkumi da yanke danyen hukunci a kan kasashe da dama, don kare moriyar kanta. Wannan bambanci a sarari ya nuna, shin wane bangare ne yake da adalci. (Bello Wang)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rundunar Sojin Haɗin Gwiwa Ta Ƙasashe Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 15 A Borno

Next Post

Me Ya Sa Lee Hsien Loong Yake Da Karfin Gwiwa Kan Makomar Kasar Sin?

Related

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

5 days ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

7 days ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

2 weeks ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

2 weeks ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

2 weeks ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Next Post
Me Ya Sa Lee Hsien Loong Yake Da Karfin Gwiwa Kan Makomar Kasar Sin?

Me Ya Sa Lee Hsien Loong Yake Da Karfin Gwiwa Kan Makomar Kasar Sin?

LABARAI MASU NASABA

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.