Mukaddashin shugaban Nijeriya, Yemi Osinbajo, ya mika wa sabbin ministocin da aka rantsar dasu sati uku da suka wuce ma’aikatu.
An rantsar da Sulaiman Hassan da Stephen Ocheni tun a watan Mayu, bayan yan majalisar dattawa sun tattance su.
Mista Ocheni shine zai maye gurbin da marigayi James Ocholi ya bari sanadiyar mutuwarsa a hadarin mota bara, dukkansu yan jihar Kogi ne, zai kama aiki a matsayin karamin minista a ma’aikatar kwadago
Sulaiman hassan shi kuma zai cike gurbin jihar Gombe ne a matsayin karamin ministan, wuta, ayyuka da gidaje.