• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Katsina: Sojoji Sun Ragargaje Su

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Sabon Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Katsina: Sojoji Sun Ragargaje Su
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani abu mai kama da sakaci da ya ɗaure kan al’umma da dama a Jihar Katsina shi ne, yadda ‘yan ta’adda suka yi wa wasu garuruwa ƙawanya suka yi masu kisan kare dangi a karamar hukumar Kankara ta Jihar Katsina.

Sai dai bayanan da suka biyo bayan wannan mummunan harin wuce gona da iri shi ne, irin yadda gwamnatin Jihar Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda ta yi gum da bakinta a daidai lokacin da radadin kisan ke tafarfasa.

  • Tinubu Ya Ba Jama’an Tsaro Umarnin Kamo Ƴan Ta’addan Da Suka Kashe Mutane A Katsina
  • Za A Yi Sallah Babu Lantarki A Jahohin Kano, Jigawa, Katsina, Ma’aikatan KEDCO Sun Shiga Yajin Aiki

Ba tare da aune ba, sai dai ji aka yi tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takara shugaban kasa a zaben da ya gabata a karkashin jam’iyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar yana jajanta wa al’ummomin da abin ya shafa, ita kuwa gwamantin Ji-har Katsina ta yi shiru.

Bullar wancan sanarwar tasa jikin jama’a da dama ya yi la’asar ganin cewa wani mutum daga nisan duniya ya fara nuna alhini kan wannan lamari, amma gwa-mantin Jihar Katsina tana nan gefe guda.

Alhaji Atiku ya ce ya yi mamakin yadda ‘yan bindiga ke da karfin halin kai wa ja-mi’an tsaro harin kwantan bauna har su kashe wasu daga ciki.

Labarai Masu Nasaba

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

Yana mai Allah wadai da kuma tir da irin wannan lamarin da ke taruwa a Jihar Katsina da wasu jihohin arewacin Nijeriya tsawon lokaci abin ya ki karewa.

Kamar yadda rahotanni suka bayyana cewa an kashe fiye da mutane 50 a hare-haren wuce gona da iri da ‘yan bindiga suka kai ciki har da jami’an ‘yansanda hudu da kuma dakarun zaman lafiya na C-Watch guda biyu.

Rundunar ‘yansandan Jihar Katsina a ta bakin mai magana da yawunta, ASP Abu-bakar Aliyu ya yi taron manema labarai, inda ya bayyana yadda abin ya faru a bangaren jami’an tsaro. Ya ce an kashe jami’an ‘yansanda 4 da jami’an C-Watch 2 da Kuma mutane 20.

Ya kara da cewa lallai wannan harin abin takaici ne da bakin ciki, musamman irin yadda harin ya fi rutsawa da mata da kananan yara.

Kazalika, rundunar ‘yansanda ta ce tuni jami’an tsaro sun yi kawaye wajen da wannan lamari ya faru domin tabbatar da an kama wadannan suka yi wannan danyen aiki domin su girbi abin da suka shuka.

Sai dai kuma a cikin wani irin yanayi da sanyin jiki gwamantin Jihar Katsina ta fitar da sanarwa tana jajanta wa al’ummomin da wannan harin ya shafa a kauyen gidan Boka a karamar hukumar Kankara, inda ta ce an kashe mutane 26.

Sanarwar wanda mai taimaka wa gwamnan Jihar Katsina kan harkokin yada laba-rai, Ibrahim Kaula ya fitar, inda ya nuna takaici da wannan harin wuce gona da iri.

Sai dai sanarwar ta zo ne bayan da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya fitar da tashi wanda ake ganin kamar gwamantin Jihar Katsina ta yi fargar jaji.

Ibrahim ya ce gwamnatin Dikko Radda a shirye take wajen ganin ta kawo karshen wannan matsalar tsaro da ta-ki-ci-ta-ki cinyewa kuma ta kara nuna bukatar da ake da ita na ganin jama’a da su ci gaba da taimaka wa jami’an tsaro da bayanai sirri domin ganin an samu nasara

Gwamna Radda dai ya sha nanata cewa ba zai taba yin sulhu da ‘yan bindiga ba, sai dai idan ‘yan bindiga sun ajiye makamansu, sun rungumi zaman lafiya.

Yanzu dai Jihar Katsina ta kara komawa wani sansanin daukar rai, inda kullum sai an kashe jama’a ko an sace, ko an kone gari da sauran nau’in zalunci ba dare ba rana.

A wani hari na ramuwar gayya kuma, rundunar sojin saman Nijeriya ta kashe ‘yan bnidiga 29 tare da ceto wadanda suka yi garkuwa da su ciki har da diyar sarkin ga-rin Ruwan Godiya.

An samu nasarar ne a wani hari ta sama da aka kai a kusa da tsaunin Bakori da Yartsintsiya a karamar hukumar Kankara ta Jihar Katsina.

Wannan farmakin ya gudana ne a matsayin na mayar da martani ga harin baya-bayan nan da aka kai a karamar hukumar Kankara a ranar Lahadi, 9 ga watan Yunin 2024, ya kuma dakile ayyukan ta’addanci a yankin.

Rundunar sojin saman Nijeriya ta bayyana cewa za ta ci gaba da hada kai da so-jojin kasa da hukumomin leken asiri don ganowa tare da kawar da masu aika ta laifuka a yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Ruwa Da Tsaki Na Bukatar A Binciki Asusun Yakin Neman Zaben LP A 2023

Next Post

Jihohi Goma Mafi Arahar Abinci A Nijeriya

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

7 minutes ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

1 hour ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

2 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

4 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

6 hours ago
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta
Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

10 hours ago
Next Post
Jihohi Goma Mafi Arahar Abinci A Nijeriya

Jihohi Goma Mafi Arahar Abinci A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.