• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Katsina: Sojoji Sun Ragargaje Su

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
in Labarai
0
Sabon Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Katsina: Sojoji Sun Ragargaje Su
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani abu mai kama da sakaci da ya ɗaure kan al’umma da dama a Jihar Katsina shi ne, yadda ‘yan ta’adda suka yi wa wasu garuruwa ƙawanya suka yi masu kisan kare dangi a karamar hukumar Kankara ta Jihar Katsina.

Sai dai bayanan da suka biyo bayan wannan mummunan harin wuce gona da iri shi ne, irin yadda gwamnatin Jihar Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda ta yi gum da bakinta a daidai lokacin da radadin kisan ke tafarfasa.

  • Tinubu Ya Ba Jama’an Tsaro Umarnin Kamo Ƴan Ta’addan Da Suka Kashe Mutane A Katsina
  • Za A Yi Sallah Babu Lantarki A Jahohin Kano, Jigawa, Katsina, Ma’aikatan KEDCO Sun Shiga Yajin Aiki

Ba tare da aune ba, sai dai ji aka yi tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takara shugaban kasa a zaben da ya gabata a karkashin jam’iyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar yana jajanta wa al’ummomin da abin ya shafa, ita kuwa gwamantin Ji-har Katsina ta yi shiru.

Bullar wancan sanarwar tasa jikin jama’a da dama ya yi la’asar ganin cewa wani mutum daga nisan duniya ya fara nuna alhini kan wannan lamari, amma gwa-mantin Jihar Katsina tana nan gefe guda.

Alhaji Atiku ya ce ya yi mamakin yadda ‘yan bindiga ke da karfin halin kai wa ja-mi’an tsaro harin kwantan bauna har su kashe wasu daga ciki.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Yana mai Allah wadai da kuma tir da irin wannan lamarin da ke taruwa a Jihar Katsina da wasu jihohin arewacin Nijeriya tsawon lokaci abin ya ki karewa.

Kamar yadda rahotanni suka bayyana cewa an kashe fiye da mutane 50 a hare-haren wuce gona da iri da ‘yan bindiga suka kai ciki har da jami’an ‘yansanda hudu da kuma dakarun zaman lafiya na C-Watch guda biyu.

Rundunar ‘yansandan Jihar Katsina a ta bakin mai magana da yawunta, ASP Abu-bakar Aliyu ya yi taron manema labarai, inda ya bayyana yadda abin ya faru a bangaren jami’an tsaro. Ya ce an kashe jami’an ‘yansanda 4 da jami’an C-Watch 2 da Kuma mutane 20.

Ya kara da cewa lallai wannan harin abin takaici ne da bakin ciki, musamman irin yadda harin ya fi rutsawa da mata da kananan yara.

Kazalika, rundunar ‘yansanda ta ce tuni jami’an tsaro sun yi kawaye wajen da wannan lamari ya faru domin tabbatar da an kama wadannan suka yi wannan danyen aiki domin su girbi abin da suka shuka.

Sai dai kuma a cikin wani irin yanayi da sanyin jiki gwamantin Jihar Katsina ta fitar da sanarwa tana jajanta wa al’ummomin da wannan harin ya shafa a kauyen gidan Boka a karamar hukumar Kankara, inda ta ce an kashe mutane 26.

Sanarwar wanda mai taimaka wa gwamnan Jihar Katsina kan harkokin yada laba-rai, Ibrahim Kaula ya fitar, inda ya nuna takaici da wannan harin wuce gona da iri.

Sai dai sanarwar ta zo ne bayan da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya fitar da tashi wanda ake ganin kamar gwamantin Jihar Katsina ta yi fargar jaji.

Ibrahim ya ce gwamnatin Dikko Radda a shirye take wajen ganin ta kawo karshen wannan matsalar tsaro da ta-ki-ci-ta-ki cinyewa kuma ta kara nuna bukatar da ake da ita na ganin jama’a da su ci gaba da taimaka wa jami’an tsaro da bayanai sirri domin ganin an samu nasara

Gwamna Radda dai ya sha nanata cewa ba zai taba yin sulhu da ‘yan bindiga ba, sai dai idan ‘yan bindiga sun ajiye makamansu, sun rungumi zaman lafiya.

Yanzu dai Jihar Katsina ta kara komawa wani sansanin daukar rai, inda kullum sai an kashe jama’a ko an sace, ko an kone gari da sauran nau’in zalunci ba dare ba rana.

A wani hari na ramuwar gayya kuma, rundunar sojin saman Nijeriya ta kashe ‘yan bnidiga 29 tare da ceto wadanda suka yi garkuwa da su ciki har da diyar sarkin ga-rin Ruwan Godiya.

An samu nasarar ne a wani hari ta sama da aka kai a kusa da tsaunin Bakori da Yartsintsiya a karamar hukumar Kankara ta Jihar Katsina.

Wannan farmakin ya gudana ne a matsayin na mayar da martani ga harin baya-bayan nan da aka kai a karamar hukumar Kankara a ranar Lahadi, 9 ga watan Yunin 2024, ya kuma dakile ayyukan ta’addanci a yankin.

Rundunar sojin saman Nijeriya ta bayyana cewa za ta ci gaba da hada kai da so-jojin kasa da hukumomin leken asiri don ganowa tare da kawar da masu aika ta laifuka a yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Ruwa Da Tsaki Na Bukatar A Binciki Asusun Yakin Neman Zaben LP A 2023

Next Post

Jihohi Goma Mafi Arahar Abinci A Nijeriya

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

4 hours ago
Katsina
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

5 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

11 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

12 hours ago
Next Post
Jihohi Goma Mafi Arahar Abinci A Nijeriya

Jihohi Goma Mafi Arahar Abinci A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Katsina

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.