• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sallar Idi Babbar Rana Ga Musulmi

by Nuhu Ubale Ibrahim
2 years ago
in Bakon Marubuci, Fatawa, Ilimi
0
Sallar Idi Babbar Rana Ga Musulmi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da sunan Allah mai Rahama mai Jin ƙaai. Yabo da godiya da kirari da girmamawa sun tabbata ga Allah Shi kaɗai. Yabon Allah da amincinsa su ƙara tabbata ga fiyayyen halitta, shugaban na farko da na ƙarshe tare alayensa da sahabbansa baki ɗaya. 

Bayan haka;
wannan rubutu ya ƙunshi bayani akan sallar idi a bisa fahimtar Mazhabar Malikiyya. Ga bayanin kamar haka:

  • Layya Babbar Ibada: Yadda Ake Gudanar Da Ita Da Matsayinta A Musulunci
  • Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

1. Sallar idi sunna ce mai ƙarfi ta wajibi.

2. Liman da mamu za su tafi filin idi bayan rana ta fito domin suna isa filin idi hantsi ya yi sai a yi salla.

3. Ana yin sallar idi a filin idi ba a masallaci ba sai dai idan akwai lalura, to za a iya yi a masallaci, haka nan waɗanda suke a garin Makka za su yi ta ne a Harami.

Labarai Masu Nasaba

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

4. Mustahabbi ne mutum ya yi wanka domin sallar idi.

5. Mustahabbi ne idan an yi wankan a tafi masallaci ba tare da ɓata lokaci ba.

6. Mustahabbi ne a yi ado a sanya turare da sababbin tufafi ga wanda yake da iko.

7. Za a tafi filin idi ana kabarbari a bayyane har a je filin idi, idan an je ba a yin nafila za a zauna a ci kaba da kabarbari har liman ya ƙaraso, sai a tsaya da kabarbari. Idan liman yana kabarbari , nan ma mamu za su yi kabarbari idan liman ya yi.

TAMBIHI: Kabarbari aka fi buƙata sama da wazi kafin liman ya zo, don Allah a bar al’umma su raya kabarbarbari a wurin idi.

8. Sallar idi raka’a biyu ce, kuma ana yin karatu a bayya ne, a raka’a ta farko ana yin kabbara bakwai har da kabbarar harama sai liman ya fara karatu, a ta biyu kuma kabbara shida har da ta mikewa. Ana karanta Fatiha da Sabbi a rakar farko a ta biyu kuma Hal’ataka ko kuma makamantansu.

9. Idan mutum bai riski wani abu tare da liman da bai aka’a ba, to, zai yi kabbara bakwai a raka’a ta farko kafin ya yi karatu, kuma zai kabbara shida a raka’a ta biyu kafin ya fara karatu kamar yadda liman ya yi.

10. Ba a yin nafila bayan an gama sallar idi.

11. Liman zai yi huɗuba guda biyu kuma zai zauna a tsakaninsu kuma ana so ya yawaita kabarbari a huɗubarsa.

12. Ana so a yi sallar layya da wuri akan ta sallar azubi, domin ana so a ci abinci kafin a tafi karamar salla, ita kuma ta layya sai bayan an dawo.

13. Kabarbari da ake so a yi, laffuzansu suna da yawa kuma za a iya yin kowanne, daga ciki akwai: Allahu Akbar Allahu Akbar La’ilaha illallahu Allahu Akbar Allahu Akbar Walillahil Hamdu.

14. Ana so a rinƙa kabarbari a bayan kowacce salla ya farilla sau uku bayan salla da kwana uku, kuma ana so a yawaita zikiri a cikinsu.

15. Mustahabbi ne ga mata da yara idan ba za su je sallar idi ba, to su yi wanka da ado da sanya sababbun kaya idan da hali.

16. Mata su guji caba ado da sanya turare idan za su idi saboda gudun fitina.

17. Makruhi ne mutum ya ƙi yin ado da kwalliyya da gayu a ranar idi wai don gudun duniya, idan kuma ya ƙi yi da sunan addini, to ya zama ɗan bidi’a.

18. Yara da mata za su iya yin wasanni a ranakun idi.

19. Mustahabbi ne mutum ya sabunta hanya wajen dawo gida, watau ya sauya hanya.

Allah ya karɓa mana ibadunmu ya gafarta mana. Amin.

Nuhu Ubale Ibrahim
Abu Razina Paki
Zul-hijja 9,1444H


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Babbar SallahSallar Idi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 4

Next Post

Shugabancin Nijeriya Na Da Matukar Wahala -Buhari

Related

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe
Ilimi

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

3 days ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

1 week ago
ASUU
Ilimi

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

1 week ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

2 weeks ago
Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Bakon Marubuci

Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

3 weeks ago
Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya
Ilimi

NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

3 weeks ago
Next Post
Shugabancin Nijeriya Na Da Matukar Wahala -Buhari

Shugabancin Nijeriya Na Da Matukar Wahala -Buhari

LABARAI MASU NASABA

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.