• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Muhammad Sanusi, ya ce, a maimakon dora laifin halin kunci da matsatsi rayuwa da ake ciki a Nijeriya ga Shugaban kasa, Bola Tinubu, zarge-zargen da tuhume-tuhumen kai har ma da nuna yatsar, ya kamata ne a yi su kan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, kan yadda ya bi wajen janyo matsaloli ga tattalin arziki.

Tsohon sarkin Kano, wanda ke jawabi ta tangaraho a ranar Lahadi a wajen wani taron addini da ya gudana a Abuja, ya ce tsohon gwamnatin da ta gabata ta kasa gudanar da tsare-tsaren da za su taimaka wa tattalin arziki.

  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta

A cewarsa, Buhari ya toshe kunnuwansa kan yadda za a bi wajen magance matsalolin da suka shafi tattalin arzikin kasar nan.

Ya ce, shi kam ba zai biye wa wasu gungun ‘yan Nijeriya da suke son ya soki Shugaban kasa Tinubu kan halin kunci da ake ciki a kasar nan ba.

Sanusi ya ce, “Tsawon shekaru na sha fada kan cewa za a fada matsalolin tattalin arziki. Dukkanin wani masanin tattalin arziki da ya fahimci yadda aka bi da tattalin arzikin kasar nan a shekaru takwas da suka wuce ya san za a iya tsintan kai cikin irin wannan mawuyacin yanayin.

Labarai Masu Nasaba

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

“Wannan kuncin rayuwa da ‘yan Nijeriya ke fuskanta, yanzu ma aka fara shiga muddin ba a dauki matakan da suka dace ba, saboda Nijeriya ba ta kasance wata kasa ta daban ba, irin wannan yanayin ya faru a Jamus, Zimbabwe, Uganda, da Benezuela.

“Tsohon gwamnati ta toshe kunnuwarta ta ki sauraron rokonmu kan matakan da za a bi a kan tsarin tattalin arziki. Na fada a gaban shugaban kasan da ke mulki a yanzu a Jihar Kaduna, cewa duk wani dan siyasan da ya gaya muku cewa abubuwa za su yi sauki, kar ma ku zabeshi, saboda karya yake muku. Mutane sun yi watsi da shawarwarinmu ne da tunanin kawai maganace ake yi ta siyasa.

“Idan zan yi adalci ga Shugaba Bola Tinubu, ba shi ne ya dace a dora wa alhakin matsatsin da ake ciki ba a halin yanzu, sama da shekaru takwas muna rayuwa ciki tsari irin ta karya da lafto basuka daga kasashen waje da ya wuce hankali.

“Ba zan shiga a dama da ni ba wajen sukar Tinubu kan matsatsin rayuwa da ake fuskanta a yanzu ba, ba wai ina cewa shi din ba zai iya yin kuskure ba ne, amma a dai wannan matsatsin da ake ciki, shugaban kasa Tinubu bai da laifi. Zan yi magana muddin na ga wani kuskure a tsarin tattalin arzikin gwamnatin Tinubu a nan gaba.” Sanusi ya shawarci masu hannu da shuni da su taimaka wa wadanda ba su da shi a halin da ake ciki tare da neman jama’a da su kara hakuri. Sannan, ya shawarci jama’a da su rage buri da dora wa kai abubuwan da ba su wajaba ba domin samun rayuwa cikin sauki da samun abincin da za a ci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Martanin Gwamnatin Tinubu Ga PDP: Matsalar Nijeriya Ba Ta Kai Ta Kasar Venezuela Ba

Next Post

Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

Related

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

8 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

12 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

13 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

14 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

16 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

19 hours ago
Next Post
Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.