ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saudiyya Ta Damke Bakin Haure Sama Da 16,000

by Sadiq
3 years ago
Saudiyya

Hukumomin Saudiyya sun ce sun kama bakin haure 16,407 da suka shiga kasar ba bisa ka’ida ba, a yankuna daban-daban cikin mako daya.

Ma’aikatar harkokin cikin gida ta kasar na cewa an kama mutanen ne bayan wani samamen hadin gwiwa da jami’an tsaro suka kaddamar a sassa daban-daban cikin wannan wata na Ramadan.

  • Gobara Ta Tashi A Wani Kamfani Da Ke Jihar Legas
  • Falala Da Takawar Da Azumin Ramadan Ya Kunsa

Kamen ya hadar da mutunen da suke zaune a kasar ba tare da izini ba, da mutunen da ba su da takardun shiga kasar, sai kuma mutunen da suka saba ka’idojin aiki na Saudiyya.

ADVERTISEMENT

Ma’aikatar ta ce ta kama wasu a lokacin da suke kokarin tsallaka kan iyakar kasar, wasu kuma an kama su ne lokacin da suke yunkurin fita daga kasar.

Ta ce kashi 74 na waɗanda aka kama, ‘yan Habasha ne, sai kashi 22 ‘yan asalin Yemen, kashi hudu kuma na sauran kasashe.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

Ma’aikatar cikin gidan ta ce an tura ‘yan ci-rani 6,251 zuwa ofisoshin jakadancin kasashensu da ke Saudiyya don samar musu takardun izini, yayin da za a mayar da mutum 10,156 zuwa kasashen da suka fito.

Ta dai gargadi duk wani mutum da ya yi sanadin shigar da wani bakon haure cikin Saudiyya ba bisa ka’ida ba, ko ya ba shi masauki, ko aiki, da dai duk wani nau’in taimako – ya tabbatar cewa zai fukanci hukuncin da zai iya kai wa daurin shekara 15 a gidan yari, matukar aka kama shi.

Sannan da biyan tarar riyal miliyan daya, idan aka same shi da laifin hada baki wajen shigar da bakin haure cikin kasar, da kuma samar musu masauki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga
Kasashen Ketare

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Next Post
Firaministan Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Singapore

Firaministan Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Singapore

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.