• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharuda 5 Da Tinubu Ya Gindaya Wa Ministocinsa

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Sharuda 5 Da Tinubu Ya Gindaya Wa Ministocinsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya umarci sabbin ministocinsa su zage damtse don kawo sauye-sauye masu kyau ga rayuwar ‘yan kasar nan.

Ya bayar da umarnin ne yayin taron majalisar zartarwarsa ta farko da ya jagoranta a ranar Litinin a fadar shugaban kasar da ke Abuja.

  • Za Mu Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci -Kwamitin Rabon Abinci A Adamawa
  • Har Yanzu Jakadan Faransa Bai Fice Daga Jamhuriyar Nijar Ba – Macron

Taron ya mayar da hankali kan cimma muradan gwamnatin Tinubu don samar da hanyoyin ci gaban tattalin arziki da wadata al’ummar Nijeriya da kuma kawo karshen talauci tare da jaddada muhimman ayyukan da ke gaban gwamnati.

Ga muhimman sharuda biyar da shugaban ya zayyana:

1. Ba za a lamunci rashin kwazo ba: Shugaba Tinubu ya kafa wani tsari da zai sa ido wajen tabbatar da rikon amana da kuma tantance ayyukan da suka rataya a kan kowane minista.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Ya ce ba zai lamunci rashin kwazo daga wurin ministocin ba.

2. Sabon Tsarin Tattalin Arziki: Shugaban ya yi kira kan samar da sabbin dabarun bunkasa kasafin kudi na cikin gida da za su mayar da hankali wajen inganta rayuwar ‘yan Nijeriya. ”

Gwamnatin ta himmatu wajen sake farfado da harkokin kudadenmu na gida don walwalar ‘yan Nijeriya,” a cewar Tinubu.

3. Ayyuka ba yawan lokacin mulki ba: Shugaba Tinubu ya jaddada cewa mukaman na ministocin ba nadi ne “yi-aiki-a-biya-ka” ba amma yana mai cewa ana auna mutuncin minista ne bisa irin ayyukan da ya yi wa kasa.

4. Dabarun samar da tsaro da ci gaban kasa: A kalaman shugaban, majalisar tana da alhakin aiwatar da manufofin da za su “gyara tattalin arzikin kasa tare da tabbatar da ci gaban hadin kai da kuma karfafa tsaro don samar da zaman lafiya da wadata a Nijeriya.”

5. Jagoranci mai sauki da karbar shawarwari: Shugaba Tinubu ya ce ya bude duk wata kofa ta karbar shawarwari don ciyar da gwamnatinsa gaba, yana mai tabbatar da cewa “a shirye nake na ba da hadin kai tare da sauraren jama’a.”

Shugaban dai ya gargade ministocin da su yi kokari tare da ba da himma wajen cimma kashin farko na ajandar da gwamnatinsa ta sa a gaba guda takwas cikin shekaru uku da ke tafe.

Ya kuma bukaci su yi aiki tukuru domin farfado da tattalin arzikin kasar saboda Nijeriya na cikin mawuyacin hali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MinistociSharudaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci -Kwamitin Rabon Abinci A Adamawa

Next Post

Zargin Bi-ta-da-ƙulli: An Hana Kotun Ɗa’ar Ma’aikata Da EFCC Da ICPC Ci Gaba Da Binciken Shugaban Yaƙi Da Rashawa Na Kano

Related

Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

14 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

20 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

21 hours ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

22 hours ago
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa
Manyan Labarai

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

23 hours ago
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

1 day ago
Next Post
Zargin Bi-ta-da-ƙulli:   An Hana Kotun Ɗa’ar Ma’aikata Da EFCC Da ICPC Ci Gaba Da Binciken Shugaban Yaƙi Da Rashawa Na Kano

Zargin Bi-ta-da-ƙulli: An Hana Kotun Ɗa'ar Ma'aikata Da EFCC Da ICPC Ci Gaba Da Binciken Shugaban Yaƙi Da Rashawa Na Kano

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.