• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Dattawan Arewa Kan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Shawarwarin Dattawan Arewa Kan Zaben 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar tuntuba na dattawan arewa (ACF) ta shawarci ‘yan Nijeriya su amince da duk wani sakamakon zaben wannan shekara domin farfado da dimokuradiyyar Nijeriya.

A cewar kungiyar, dole ne a samu wadanda suka yi nasara da kuma wadanda suka fadi, inda ta jaddada cewa ko ta yaya aka bi, ka da wani ya yi yunkurin rashin tayar da zaune tsaye ta hanyar tayar da hankulan ‘yan Nijeriya da sakamakon zaben.

  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Warware Rikici Cikin Lumana Ta Hanyarta
  • Sin Ta Yi Kira Ga Al’ummar Kasa Da Kasa Da Ta Kara Mai Da Hankali Kan Batun Somaliya

A wata sanarwa da babban sakataren kungiyar, Malam Murtala Aliyu ya fitar, ta ce duk wani yunkuri na kin amincewa da sakamakon zaben, zai zama wani mummunan farmaki ga dimokuradiyyar kasar nan, amincewa da zaben yana daya daga cikin ginshiki na tsarin dimokuradiyya.

Sanarwar ta bayyana cewa, “Kudirin ‘yan Nijeriya na kammala zaben 2023 cikin nasara bai taba shiga cikin shakku ba. Idan aka yi la’akari da duk abin da aka cimma, babu wani dalili da zai sa wani ya yi yunkurin yin kutse ga jadawalin zabe da aka sanar. Wannan ba zai zama abin karba kwata-kwata ba.”

Kungiyar dattawan arewa ta bukaci shugabanni a dukkan matakai da su dauki matakan tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin daukacin ‘yan kasa da na kasashen waje a yankunansu gabanin zabe da lokacin zabe da kuma bayan zabe, inda ta ce ‘yan Nijeriya su tabbatar da an samu zaman lafiya da lumana daga gwamnatin farar hula zuwa wata gwamnatin ta farar huda.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Haka kuma kungiyar ta shawarci kafafen yada labarai da su taka rawar gani wajen kawar da duk wani tashin hankali da ka iya tasowa lokacin bayyana sakamakon zabe.

ACF ta bayyana farin cikinta da bullo da fasahar sadarwa a harkar zabe, inda ta jaddada cewa mataki ne da ya dace da zai tabbatar da magance magudin zabe da aka saba a baya da kwace akwatin zabe da kuma sauya sakamakon zabe.

Kungiyar ta yi imanin cewa watsa sakamakon zabe ta yanar gizo daga wuraren zabe zuwa cibiyoyin tattara sakamakon zabe da kuma samar da kayayyakin da mutane za su rika sanya ido kan sakamakon zabe ta yanar gizo abubuwa ne da za su tabbatar da cewa ba a tafka magudi a zaben ba.

Sanarwar ta yaba wa kokarin Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) na samar da yanayi mai kyau da zai tabbatar da an gudanar da zabe cikin gaskiya da adalci, kuma duk kuri’un da aka kada a kasar nan za a kirga.

Kungiyar ta shawarci masu kada kuri’a da su yi la’akari da bayyanannun manufofin jam’iyya da kuma halaye da tarihin ‘yan takara.

Ta shawarci ‘yan Nijeriya da su kada kuri’unsu bisa la’akari da kabilanci, addini ko yanki, inda ta jaddada cewa ya kamata su nemi shugabannin da suka fi dacewa da muradun kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaNagartaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Zaben 2023 Zai Bambanta Da Sauran Zabukan Nijeriya

Next Post

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.