ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Dattawan Arewa Kan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Arewa

Kungiyar tuntuba na dattawan arewa (ACF) ta shawarci ‘yan Nijeriya su amince da duk wani sakamakon zaben wannan shekara domin farfado da dimokuradiyyar Nijeriya.

A cewar kungiyar, dole ne a samu wadanda suka yi nasara da kuma wadanda suka fadi, inda ta jaddada cewa ko ta yaya aka bi, ka da wani ya yi yunkurin rashin tayar da zaune tsaye ta hanyar tayar da hankulan ‘yan Nijeriya da sakamakon zaben.

  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Warware Rikici Cikin Lumana Ta Hanyarta
  • Sin Ta Yi Kira Ga Al’ummar Kasa Da Kasa Da Ta Kara Mai Da Hankali Kan Batun Somaliya

A wata sanarwa da babban sakataren kungiyar, Malam Murtala Aliyu ya fitar, ta ce duk wani yunkuri na kin amincewa da sakamakon zaben, zai zama wani mummunan farmaki ga dimokuradiyyar kasar nan, amincewa da zaben yana daya daga cikin ginshiki na tsarin dimokuradiyya.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta bayyana cewa, “Kudirin ‘yan Nijeriya na kammala zaben 2023 cikin nasara bai taba shiga cikin shakku ba. Idan aka yi la’akari da duk abin da aka cimma, babu wani dalili da zai sa wani ya yi yunkurin yin kutse ga jadawalin zabe da aka sanar. Wannan ba zai zama abin karba kwata-kwata ba.”

Kungiyar dattawan arewa ta bukaci shugabanni a dukkan matakai da su dauki matakan tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin daukacin ‘yan kasa da na kasashen waje a yankunansu gabanin zabe da lokacin zabe da kuma bayan zabe, inda ta ce ‘yan Nijeriya su tabbatar da an samu zaman lafiya da lumana daga gwamnatin farar hula zuwa wata gwamnatin ta farar huda.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Haka kuma kungiyar ta shawarci kafafen yada labarai da su taka rawar gani wajen kawar da duk wani tashin hankali da ka iya tasowa lokacin bayyana sakamakon zabe.

ACF ta bayyana farin cikinta da bullo da fasahar sadarwa a harkar zabe, inda ta jaddada cewa mataki ne da ya dace da zai tabbatar da magance magudin zabe da aka saba a baya da kwace akwatin zabe da kuma sauya sakamakon zabe.

Kungiyar ta yi imanin cewa watsa sakamakon zabe ta yanar gizo daga wuraren zabe zuwa cibiyoyin tattara sakamakon zabe da kuma samar da kayayyakin da mutane za su rika sanya ido kan sakamakon zabe ta yanar gizo abubuwa ne da za su tabbatar da cewa ba a tafka magudi a zaben ba.

Sanarwar ta yaba wa kokarin Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) na samar da yanayi mai kyau da zai tabbatar da an gudanar da zabe cikin gaskiya da adalci, kuma duk kuri’un da aka kada a kasar nan za a kirga.

Kungiyar ta shawarci masu kada kuri’a da su yi la’akari da bayyanannun manufofin jam’iyya da kuma halaye da tarihin ‘yan takara.

Ta shawarci ‘yan Nijeriya da su kada kuri’unsu bisa la’akari da kabilanci, addini ko yanki, inda ta jaddada cewa ya kamata su nemi shugabannin da suka fi dacewa da muradun kasar nan.

Arewa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Arewa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.