• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabar NIS Ta Bukaci Jami’an Tsaro Su Hada Kai Don Kula Da Iyakokin Nijeriya 

by Sadiq
2 years ago
NIS

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Caroline Wura-Ola Adepoju, ta yi kira da a ci gaba da hadin gwiwa a tsakanin hukumomin tsaro don kare iyakokin Nijeriya.

Ta ce ba za a yi watsi da horas da jami’an tsaro ba musamman a yanzu da kalubalen da suka hada da safarar makamai, fashi da makami da sauran munanan dabi’u da ka iya kawo cikas ga tsaron al’ummar kasar nan ke kara ta’azzara.

  • Jami’ai 3 Da Sojoji 22 ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Neja -DHQ
  • Sojojin Nijar Na Neman Goyon Bayan Kasashe Daban-Daban

Adepoju ta bayyana haka ne a jiya a hedikwatar hukumar a Abuja.

Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, DCI Aridegbe Adedotun ya fitar, ta bayyana cewa shugabar NIS, ta ce ziyarar da mahalarta taron inganta tsaro 27 suka kai mata wani bangare ne na inganta alaka a tsakaninsu.

Ta ce, “Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya ta kasu gida biyu: tsaron kan iyaka da kula da shige da fice. Amintacciyar iyaka kasa ita samar da tsaro, bukatar NIS shi ne samar da tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

“Kuma tabbas tsaro hakki ne na kowa da kowa, musamman ma kowace hukumar tsaro, shi ya sa aka samar da wannan kwas na tsaro.

“Yayin da ake fama da matsalar rashin tsaro a Nijeriya, fasa-kwaurin makamai, ‘yan fashi da makami, ta’addanci, fadace-fadacen makiyaya da manoma, da safarar kudade da kuma munanan dabi’u, wannan shi ne lokacin da ya dace a bai wa jami’a horo.”

Da yake jawabi a madadin mahalarta taron, mataimakin Kwanturola na Hukumar Kwastam ta Nijeriya, Abubakar Dalhatu Zurumi, ya ce cibiyar ta sauya tunaninsu inda suka samu ilimi da kwarewa a wasu bangarori.

Ya ce bukatar hada kai kan kula da iyakoki da tsaro na da muhimmanci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

October 25, 2025
Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin
Manyan Labarai

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe

October 25, 2025
Next Post
Gobarar Tsibirin Maui Ta Bata Amincewar Da Jama’a Suka Yi Da Gwamnatin Amurka

Gobarar Tsibirin Maui Ta Bata Amincewar Da Jama’a Suka Yi Da Gwamnatin Amurka

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

October 25, 2025
Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.