Rundunonin sojojin ruwan kasar Sin da na Rasha sun shirya gudanar da atisayen soji, da sintiri na hadin gwiwa a sassan ruwa da sararin sama, nan gaba cikin wannan wata na Yuli, a kusa da birnin Qingdao dake lardin Shandong na gabashin kasar Sin.
Wata sanarwa da ma’aikatar tsaron kasar Sin ta fitar a Lahadin nan, ta tabbatar da shirin gudanar da atisayen mai lakabin “Joint Sea-2026”.
Ta kuma ce bayansa, wasu dakarun kasashen biyu za su aiwatar da sintiri a wasu yankuna masu nasaba dake kan tekun Fasifik.Ma’aikatar ta kuma ce atisayen, wani bangare ne na shirin hadin gwiwa na shekara-shekara tsakanin dakarun sojin kasashen biyu, wanda ke da nufin hadin gwiwa don tunkarar tarin kalubalen tsaro, da tabbatar da yanayin zaman lafiya da daidaito a yankin. (Saminu Alhassan)













